"A Nemo Mun Ita: Bidiyon Wata Yar Makaranta Tana Sallah a Kan Hanya Ya Dauka Hankalin Jama'a

"A Nemo Mun Ita: Bidiyon Wata Yar Makaranta Tana Sallah a Kan Hanya Ya Dauka Hankalin Jama'a

  • Jama'a sun yi cece-kuce kan bidiyon wata yarinyar musulma sanye da kayan makaranta tana sallah a titi
  • Yarinyar ta yi amfani da jakarta wajen kare gabanta saboda masu wucewa, inda tayi sujjada a kansa yayin da take bin jam'in sallar da ke tashi a lasifika
  • Yayin da jajircewarta kan addininta ya taba zukata da dama, wasu sun nuna damuwa dangane da abun da ta aikata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Aisha Musa ta shafe tsawon shekaru tana kawo labaran Hausa a bangaren siyasa, tsegumi da al’amuran yau da kullum

A cikin wani bidiyo da yadu, an gano wata yarinya musulma tana sallah sanye da kayan makaranta a titi.

Yarinyar wacce alamu suka nuna tana a hanyarta ta dawowa daga makaranta ne ta tsuma zukata da jajircewarta kan addini.

Yar Makaranta tana sallah
"A Nemo Mun Ita: Wata Yar Makaranta Tana Sallah a Kan Hanya Ya Dauka Hankalin Jama'a Hoto: @sarhmymoore
Asali: TikTok

A cikin bidiyon, yarinyar ta yi amfani da jakar makaranta don kare gabanta daga masu tafiya, kuma bata damu da mutanen da ke wucewa ba.

Kara karanta wannan

"Ku nemo min ita": Bidiyon wata daliba tana sallah a kan hanya ya dauki hankulan jama'a

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ta yi sujjada kan jakar yayin da take bin jam'in sallar da ke tashi daga wani masallaci

Shafin @sarhmymoore ne ya wallafa bidiyon a TikTok kuma an samu mutane fiye da 186k da suka kalla a daidai lokacin kawo rahoton nan.

Kalli bidiyon a kasa:

Jama'a sun yi martani

konibaje3 ya ce:

"Na rantse sai da hawaye ya zuba daga idanuna. Me zai haka ka karbar Allah? Allah Ya albarkace ta."

Haykay_Global ya ce:

"Don Allah ku nemo mun wannan yarinyar zan bata 50k."

nafiudanladi480 ya ce:

" Allah madaukakin sarki ya amsa ibadunmu ya ku yan uwana, don Allah kada ku ga laifinta..."

Senior Man ya ce:

"Duk da cewar ni Kirista ne, na sani a cikin raina Allah ya karbi addu'arki yar'uwata, abun alkhairi ne ka daraja mahaliccinka."

Kara karanta wannan

"Ba su gane shi ba": Hamshakin mai kudi Femi Otedola ya shiga motar haya a wani tsohon bidiyo

Babban fasto zai gina katafaren masallaci

A wani labari na daban, Shugaban cocin INRI Evangelical Spiritual, Primate Ayodele, ya sanar da aniyarsa na gina katafaren masallaci na miliyoyin naira a jihar Legas.

Mai ba shi shawara kan harkokin labarai, Osho Oluwatosin ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya gabatarwa manema labarai, a ranar Alhamis, 18 ga watan Janairu, Nigerian Tribune ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Online view pixel