Musulmai Sun Yaba Wa Yan Kabilar Ibo da Suka Gudanar da Karamar Sallah a Enugu

Musulmai Sun Yaba Wa Yan Kabilar Ibo da Suka Gudanar da Karamar Sallah a Enugu

  • Wasu Musulmai 'yan kabilar Igbo sun ja hankalin mutane da yawa a soshiyal midiya ganin yadda suka yi ƙaramar Sallah
  • Da yawan Musulmai a Tuwita sun nuna mamakinsu da ganin Musulunci ya shiga har cikin inyamurai a Najeriya
  • A ranar Jumu'a 21 ga watan Afrilu, Musulman Najeriya suka gudanar da Eid-el-Fitr bayan ganin jinjirin watan Shawwal

Enugu - Mabiya addinin Musulunci 'yan kabilar Ibo da suka yi Sallah ƙarama a jihar Enugu sun sha yabo daga yan uwansu a shafin sada zumunta Tuwita.

Hakan ta faru ne bayan bidiyo ya watsu a Tuwita, inda aka ga wani mutumi, Siraj Nwansukka, ya jagorancin sauran jama'a kuma ya yi huɗuba a harshen Ibo ranar Jummu'a.

Filin idi.
Musulmai Sun Yaba Wa Yan Kabilar Ibo da Suka Gudanar da Karamar Sallah a Enugu Hoto: punchng
Asali: UGC

Punch ta ce an ɗauki bidiyon Nwansukka ranar 21 ga watan Afrilu, 2023 daidai da 1 ga watan Shawwal, 1444AH a filin idi na garin Alor-Agu, wanda Musulmai suka fi rinjaye, ƙaramar hukumar Eze ta kudu, jihar Enugu.

Kara karanta wannan

Eid-Al-Fitr: An Ga Jinjirin Watan Karamar Sallah Shawwal 1444/2023 a Saudiyya

Zuwa yanzu akalla mutane 2000 suke tura bidiyon ga abokanansu, sama da 200 suka tofa albarkacin bakinsi yayin da fiye da 5,000 suka kalli bidiyon.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Martanin mutane a soshiyal midiya

Mudashiru Temitope ya ce:

"Karo na farko kenan da na ga Ibo musulmai, gunin sha'awa, Masha Allah, muna fatan Allah ya karbi ibadunmu."

Wata Amaka Ogili ta rubuta cewa:

"Kawuna ya mutu a cikin addinin Musulunci, duk ɗaya muke bamu nuna wa juna wariya."

Yayin da yake nuna mamakin da ya shiga bayan ganin bidiyon, Daddy Evra ya ce:

"Wai dagaske? Na kasa yarda da abinda nake gani, ko kunsan ina yawan tunani a kan haka? A takaice dai akwai Ibo musulmai? Allahu Akbar."

A wani martanin kuma, Phanini ya ce, "Karo na farko kenan da naga Musulmai yan ƙabilar Ibo."

Kara karanta wannan

Allah Ya Kawo Mu: Muhimman Abubuwa 7 da Ya Kamata Ku Sani Game Da Ƙaramar Sallah

Wani mai suna Abdul-Afeez ya kara da cewa:

"Maganar gaskiya wannan sabon abu ne a wurina amma fa duk da haka ban yi mamaki ba saboda abinda Allah ya faɗa a cikin littafinsa mai tsarki Alƙur'ani."

Wani Mutumi Ya Daɓa Wa Lamami Wuka

A.wani labarin kuma Mutumi Ya Daɓa Wa Lamami Wuka Ana Tsaka da Sallar Asuba a Cikin Watan Azumi

An tattaro cewa mutumin ya kutsa kai lokacin da aka tafi Sujjada, ya shiga har wurin liman ya caka masa wuƙa sau biyu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel