Orji Kalu: Tsohon Gwamna Kuma Fitaccen Sanatan APC Ya Yi Babban Rashi a Iyalansa

Orji Kalu: Tsohon Gwamna Kuma Fitaccen Sanatan APC Ya Yi Babban Rashi a Iyalansa

  • Kowane rai zai ɗanɗani ɗacin mutuwa, Allah ya yi wa matar Sanata Orji Uzo Kalu, rasuwa tana da shekara 61 a duniya
  • Kalu, tsohon gwamnan jihar Abiya da ke kudu maso gabashin Najeriya ne ya sanar da rasuwar uwar gidansa a shafinsa
  • Ya ce ta kasance mutumiyar kirki mai bautar Allah kuma za'a gudanar da bikin tunawa da ita a ƙasae Amurka

Abia - Tsohon gwamnan jihar Abiya da ke kudu maso gabashin Najeriya, Sanata Orji Kalu, ya sanar da mutuwar uwar gidansa, Misis Ifeoma Kalu.

A wata sanarwa da ya rattaɓa wa hannu kuma aka wallafa a shafinsa na Facebook, Kalu ya ce matarsa ta farko ta koma ga mahaliccinta tana da shekaru 61 a duniya.

Orji Kalu.
Orji Kalu: Tsohon Gwamna Kuma Fitaccen Sanatan APC Ya Yi Babban Rashi a Iyalansa Hoto: Orji Ƙalu
Asali: UGC

Tsohon gwamnan kuma mai tsawatarwa a majalisar dattawa 'Chief Whip' ya ce marigayya Ifeoma mace ce mai nagarta, wacce ta sadaukar da kanta wajen bauta wa Allah da taimakon mutane.

Kara karanta wannan

Abu Ya Girma: Miyagun Yan Daba Sun Kusa Sheƙe Ɗan Takarar Gwamnan APC a 2023

Sanatan ya bayyana cewa za'a gudanar da bikin tunawa da marigayyar na musamman domin girmamawa a ƙasar Amurka.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A sanarwan da ya wallaha a shafinsa, Sanata Kalu ya ce:

"Cikin nauyin zuciya da raɗaɗi mai zafi, muna sanar da mutuwar Misis Ifeoma Ada Kalu, mai kimanin shekaru 61 a duniya."
"Ta kasance mace ta gari a zamanin rayuwarta, wacce ta sadaukar da kanta wajen bauta wa Allah da taimaka wa al'umma. An shirya gudanar da bikin tuna wa da ita a ƙasar Amurka."
"Dan Allah ku riƙa sanya ta a Addu''inku da sauran abokai da masoyan da suka tafi suka barmu a wannan lokacin mai wahalar jurewa. Muna fatan ranta ya samu salama."

Sanata Orji Kalu na cikin shugabanni a majalisa da ke hangen kujerar shugaban majalisar Dattawa a majalisa ta 10 da ake dab da rantsarwa.

Kara karanta wannan

Innalillahi: 'Yan bindiga sun harbe shugaban APC a wata jiha, sun hallaka mazauna kauye

Yan ta'addan IPOB sun sheka barzahu a Abiya

A wani labarin na daban kuma Yan Ta'adda da Dama Sun Mutu Yayin da Suka Kaiwa Yan Sanda Hari a Abia

Rundunar yan sandan jihar Abiya ta ce jami'anta sun samu nasarar dakile yunkurin mambobin ƙungiyar 'yan awaren IPOB, sun sheƙe 5.

A wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce mambobin ƙungiyar sun yi yunkurin kaiwa 'yan sanda hari amma mummunan nufin ya koma kansu.

Asali: Legit.ng

Online view pixel