Cikakken Jerin Yan Kwallon Da Ba Zasu Samu Damar Taka Leda a World Cup Ba Saboda Injury

Cikakken Jerin Yan Kwallon Da Ba Zasu Samu Damar Taka Leda a World Cup Ba Saboda Injury

Yayinda ake saura kwanaki goma (10) kacal da fara gasar kwallon duniya a kasar Qatar, wasu shararrun yan kwallo ba zasu samu damar taka ledar ba saboda raunuka da suka samu.

Gasar kwallon duniyar bana na cike da tarihi da dama.

Wannan shine karon farko da za'a buga gasar a kasar Larabawa sannan kuma karon farko da za'a buga a karshen shekara kuma tsakiyar kakar kwallon kungiyoyin kwallo.

Sakamakon haka, yan kwallo da dama sun samu raunuka yayinda suke takawa kungiyoyinsu kwallo.

A baya da ake buga gasar a tsakiyar shekara tsakanin Yuni da Yuli, yan kwallo na da hutun makonni don murmurewa daga ciwukan da suka samu.

Maney
Cikakken Jerin Yan Kwallon Da Ba Zasu Samu Damar Taka Leda a World Cup Ba Saboda Injury Hoto: Sadio Mane
Asali: Depositphotos

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ga jerin yan kwallon da ba zaku gani a Qatar ba

Kara karanta wannan

Sojoji Sun Bindige Kwamandojin IPOB 13, Sun Kwato Makamai Da Kayayyakin Aikin INEC

Yan KwalloKasarsu
Sadio Mane Senegal
Paul Dybala Argentina
Romelu Lukaku Belgium
Mike MaignanFaransa
Paul Pogba Faransa
N’Golo Kante Faransa
Timo Werner Jamus
Diogo Jota Portugal
Georginio Wijnaldum Netherlands
Diego Carlos Brazil
Arthur Melo Brazil
Ben Chilwell Injila
Reece JamesInjila
Jesus ‘Tecatito’ CoronaMexico
Florian Wirtz ()Jamus
Kamaldeen Sulemana Ghana
Sardar Azmoun Iran
Raul Jimenez Mexico
Dusan Vlahovic Serbia
Son Heung-min Koriya Ta Kudu
Yann Sommer Switzerland
Ronald Araujo Uruguay
Joe Allen Wales
Giovani Lo Celso Argentina
Raphael Varane Faransa

2022 World Cup: Zina haramun ne, Gwamnatin Qatar gargadi masu zuwa

Gwamnatin kasar Qatar ta gargadi duk ami niyyar halartan gasar kwallon duniya da zai gudana a kasar Qatar bana cewa wanda aka kama kebance da wata budurwa ba matarsa zai kwashe shekaru bakwai a magarkama

Kara karanta wannan

Sauya Fasalin Naira: Miyetti Allah Ta Roki CBN Ya Kara Wa'adi Saboda Kada Fulani Suyi Hasara

Gwamnati ta kara da cewa haramun ne shan giya a bainar jama'a a Qatar.

Qatar ta bayyana cewa ko kwayar zarra ba zata canza dokokinta na addinin Islama ba don wani gasar kwallo na kwanaki 21 kacal.

A cewar DailyStar:

"Idan ba miji da mata masu aure ba, basu yarda mutum yayi jima'i ba. Hakazalika babu casu gaba daya. Kowa ya fahimci haka ko kuma a jefashi kurkuku."
"Yan kallo su shirya, babu jima'i da zinace-zinace wannan karon."

Zina, Luwadi da Madigo haramun ne a kasar Qatar, duk wanda aka kama zai iya sha daurin shekaru 7 a gida yari.

Asali: Legit.ng

Online view pixel