Gwamna Wike Ya Rantsar Da Sabbin Hadimai 100,000 Da Ya Nada

Gwamna Wike Ya Rantsar Da Sabbin Hadimai 100,000 Da Ya Nada

  • Gwamna Nyesom Wike ya cika alkawarinsa na nada hadiman siyasa na musamman guda dubu dari
  • Wike ya yi wadannan nade-nade ne a makonnin da suka gabata kuma aikinsu daya; kare kuri'un PDP a 2023
  • Yan Najeriya sun bayyana mabanbantan ra'ayi kan wannan nadi da gwamna Wike yayi

Port Harcout - Gwamnan jihar Rivers, Nyesom Wike, ya rantsar da bari na farko na sabbin hadimai 100,000 da ya nada kan harkokin zabe wadanda zasu yi masa aiki a zaben 2023.

A taron da ya jagoranta ranar Alhamis, Wike ya rantsar da hadiman da zasu aiki a mazabun Kudu maso gabashin Rivers da Kudu maso yammacin jihar.

Wikey
Gwamna Wike Ya Rantsar Da Sabbin Hadimai 100,000 Da Ya Nada Hoto: @GovWike
Asali: Twitter

Gwamnan da kansa ya bayyana hakan a shafinsa na Tuwita.

Yace:

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Kara karanta wannan

2023: Nasarar APC Na Cikin Haɗari, In Ji Shugaban Kamfen Na Adamawa

"A Yau na rantsar da bari na farko na sabbin hadiman lamuran siyasa 100,000 da na nada a Kudu maso gabashin Rivers da Kudu maso yammacin Rivers."

Ana Saura Yan Watanni Ya Sauka: Nade-Nade Da Wike Yayi

Ana saura watanni takwas karewar wa'adin mulkinsa matsayin gwamna, Nyesom Wike na Rivers ya yi manyan nade-nade na dubunnan mutane lokaci guda.

Wannan ya biyo bayan rikice-rikicen da ke gudana tsakanin gwamnan da uwar jam'iyyarsa ta Peoples Democratic Party PDP.

A cikin wata guda kadai, Wike ya nada mutum kimanin dubu saba'in don kare muradun zaben da za'ayi a 2023.

A mukaman da ya bada, Wike ya sanya mutane a kowani lungu da sakon jihar don tsare masa akwatin zaben jiharsa gaba daya.

Bayan wadannan nade-nade, Wike dai ya bayyana cewa muddin ya raba jiha da jam'iyyar PDP babu yadda za'a yi ta lashe zabe.

Asali: Legit.ng

Online view pixel