Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya dira birnin Lisbon, kasar Portugal

Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya dira birnin Lisbon, kasar Portugal

  • Shugaba Muhammadu Buhari ya isa kai ziyarar aiki kasar Portugal bisa gayyatar Shugaba Marcelo Rebelo de Sousa
  • Yayin ziyarar aikin, za a karrama Shugaba Buhari da lambar yabo ta ‘Great Collar of the Order of Prince Henry’
  • Buhari zai gana da farai ministan kasar, Antonio Costa, shugaban majalisa Dr Augusto Santo Silva da yan Najeriya mazauna Portugal

Lisbon - Shugaba Muhammadu Buhari dira Lisbon, babb birbirnin kasar Portugal lafiya a ranar Talata, 28 ga Yunu, 2022.

Buhari Sallau, hadimin shugaban kasan ya bayyana hakan a gajeren jawabi da hotunan da ya fitsr a shafinsa na Facebook.

Yace:

”Shugaba Muhammadu Buhari ya isa Lisbon, Portugal don ziyara tare da halartar taron teku na majalisar dinkin duniya.”

Kalli hotunan:

Kara karanta wannan

Babban ɗan shugaban Dattawan Arewa, Farfesa Ango Abdullahi, ya rasu

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Lisbon
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya dira birnin Lisbon, kasar Portugal Hoto: Buhari Sallau
Asali: Facebook

Kisbom
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya dira birnin Lisbon, kasar Portugal Hoto: Buhari Sallau
Asali: Facebook

Lisbon
Yanzu-yanzu: Shugaba Buhari ya dira birnin Lisbon, kasar Portugal
Asali: Facebook

Wadanda za su yi wa Buhari rakiya

Wadanda za su raka Buhari a tafiyar sun hada da Ministan Harkokin wajen Najeriys, Geoffrey Onyeama; Ministan Labarai da Al'adu, Lai Mohammed; Ministan Masana'antu, Kasuwanci da Saka Hannun Jari, Adeniyi Adebayo; Ministan Matasa da Wasanni, Sunday Dare da Ministan Sadarwa da Tattalin arzikin zamani, Isa Pantami.

Saura sun hada da NSA, Manjo Janar Babagana Monguno (mai ritaya); Direkta Janar na NIA, Amb. Ahmed Rufa’i Abubakar da Shugaban NiDCOM Honorable Abike Dabiri-Erewa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdul Rahman Rashid avatar

Abdul Rahman Rashid Rashidah Abdul Rahman 'yar jarida ce kuma dalibar ilimi wacce ta kwashe shekaru kimanin hudu yanzu tare da shararriyar jarida Legit. Ta samu gogewa a ɓangaren rubutun labarai akan fannoni shatta, wanda suka hada da siyasa, kasuwanci, wasanni, nishadi, dss. Zaku tuntubarta a akwatin email: abdulrahman.rashidah@corp.legit.ng