Yadda muka lallasa APC a zaben Abuja, haka zamuyi mata a 2023: PDP

Yadda muka lallasa APC a zaben Abuja, haka zamuyi mata a 2023: PDP

  • Jam'iyyar adawa ta PDP ta lallasa APC a addadin kujerun kansila a zaben da ya gudana a birnin tarayya
  • A zaben ciyamomi kuwa, an yi kunnen jaki; PDP ta lashe uku, jam'iyyar APC ta samu lashe uku
  • Mafi takaici ga APC shine karamar hukumar Kuje inda PDP ta lashe dukkan kujerun goma

Abuja - Jam'iyyar Peoples Democratic Party (PDP) ta bayyana farin cikin bisa nasarar da ta samu a zaben kananan hukumomin birnin tarayya Abuja da ya gudana karshen makon da ya gabata.

Kakakin jam'iyyar, Hon. Debo Ologunagba, a jawabin da ya saki ya bayyana cewa wannan nasara da PDP ta samu a Abuja na nuna yadda zasuyi nasara a 2023.

An gudanar da zabe a kananan hukumomin Abuja shida wanda ya hada da AMAC, Bwari, Abaji, Kuje, Gwagwalada, da Kwali.

Kara karanta wannan

Ku taimaka ku sake damƙa amanar Najeriya hannun APC a 2023, Lawan ya roki yan Najeriya

Yace:

"Nasarar da Peoples Democratic Party (PDP) ta samu a kananan hukumomi uku; masu suna AMAC, Bwari da Kuje..yan nuna yadda mutane ke son mulki ya koma hannun PDP a 2023."
"Tunda aka zabi PDP ta jagoran karamar hukumar AMAC wacce ke cikin gari, yan Najeriya sun nuna cewa lallai sun yanke shawara fitittikan APC a 2023."

Jam'iyyarPDP
Yadda muka lallasa APC a zaben Abuja, haka zamuyi mata a 2023: PDP Hoto: Offical PDP
Asali: Facebook

Asali: Legit.ng

Online view pixel