Za ayi sulhu tsakanin Bola Tinubu da wanda ya kai shi kotu da zargin satar Naira Biliyan 20

Za ayi sulhu tsakanin Bola Tinubu da wanda ya kai shi kotu da zargin satar Naira Biliyan 20

  • Dapo Apara ya shigar da karar Bola Tinubu, yana zarginsa da satar kudi daga kamfanin Alpha Beta
  • Tsohon shugaban na Alpha Beta ya na zargin Tinubu da hannu a tsige shi saboda bankado asirinsa
  • Lauyan da Apara ya dauka haya, Ebun-Olu Adegboruwa ya nuna za su janye karar da aka shigar

Lagos - Tsohon babban manajan kamfanin Alpha Beta Consulting, Dapo Apara, Bola Tinubu da Akin Doherty, za su sasanta a maimakon cigaba da shari’a a kotu.

A halin yanzu Akin Doherty shi ne shugaban kamfanin, kuma har da shi ake shari’a a gaban kotu.

Punch ta kawo rahoto a ranar Talata, 19 ga watan Junairu, 2022 wanda ya nuna cewa za a janye karar da aka shigar, domin a sasanta ba tare da Alkali ta shiga ba.

Kara karanta wannan

EFCC ta na binciken mutum 5 a cikin masu neman hawa kujerar Shugaban jam’iyyar APC

Lauyan wanda ya shigar da kara, Ebun-Olu Adegboruwa SAN ya bayyana wannan a lokacin da aka yi zaman kotun a filin Tafawa Balewa Square da ke garin Legas.

Mun sanar da Tinubu - Lauya

Adegboruwa SAN ya shaidawa Alkalin babban kotun cewa an je an sanar da Bola Tinubu game da wannan shari’a har gidansa a ranar 24 ga watan Nuwamba, 2021.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Bola Tinubu
Tsohon gwamnan Legas, Bola Tinubu Hoto: guardian.ng
Asali: UGC

Bola Tinubu ya samu labari ne ta sakon DHL da aka kai gidansa da ke titin Bourdillon a Ikoyi, Legas. Kotu ta kuma tabbatar da wannan ikirari da lauyan ya yi.

...amma za mu sasanta a waje

Adegboruwa ya kuma shaidawa Alkali mai shari’a sun zauna da sauran lauyoyin da ake wannan shari’a da su, da nufin a samu maslaha ba tare da an yi shari’ar ba.

A karshe an cin ma matsaya kamar yadda lauyan ya shaidawa kotu a zaman da aka yi a jiya.

Kara karanta wannan

Mai shari'a ta caccaki DSS, ta ce ka da su kara kawo Nnamdi Kanu gaban kotu da kaya daya

Rahoton ya ce babu mamaki wannan maslaha da aka samu ne ya sa ba a ga wanda ake kara da lauyoyinsu a cikin kotu yayin da aka zo domin sauraron karar ba.

Aishat Opesanwo ta dage kara

Lauyan ya bukaci a kara masu lokaci domin su kammala magana. Tuni dai mai shari’a, Aishat Opesanwo ta amince da wannan bukata, ta daga wannan sharia.

Opesanwo ta ce za a dawo kotu a ranar 24 ga watan Maris, 2022 domin jin matakin da za a dauka.

Hawa na mulki ikon Allah ne - Osinbajo

Kwanaki aka ji Yemi Osinbajo yana cewa abin da ya faru da shi a 2015 ikon Allah ne, domin ba zai iya lashe zaben karamar hukuma ba, sai ga shi a fadar shugaban kasa.

Osinbajo ya ce ya na otel da abokan aikinsa, su na shirya kara da za a shigar a kotun koli, kwatsam sai aka kira shi a waya cikin dare, daga nan kuma sai labari.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Hadimin Buhari ya bayyana adawarsa ga tsayawar Tinubu takarar shugaban kasa

Asali: Legit.ng

Online view pixel