Idan Buhari na son zaman lafiya ya saki Nnamdi Kanu a shekarar nan, Ohaneaze Ndigbo

Idan Buhari na son zaman lafiya ya saki Nnamdi Kanu a shekarar nan, Ohaneaze Ndigbo

Kungiyar kare muradun kabilar Igbo a Najeriya, Ohanaeze Ndigbo ta lashi takobin kauraewa zaben 2023 muddin Shugaba Muhammadu Buhari bai saki Nnamdi Kanu a shekarar 2022 ba.

Kungiyar ta yi kira ga Shugaban kasan ya saki Nnamdi Kanu muddin yana son zaman lafiya ya dawo a yankin kudu maso gabas.

Kungiyar ta yi wannan kira ne a jawabin sabon shekarar da ta saki ranar Asabar ta hannun Sakataren Janar din ta, Okechukwu Isiguzoro.

A jawabin, ya bayyana cewa shi kanshi Buhari ya san sakin Nnamdi Kanu na da muhimmanci wajen wanzuwar zaman lafiya a yankin.

Yace:

"Shugaba Muhammadu Buhari ya taimaka ya saki Nnamdi Kanu a 2022 don samar da zaman lafiya, tsaro, da nutsuwa a yankin kudu maso gabashin Najeriya."

Kara karanta wannan

Yanzu nan: Shugaban kasa Buhari da Jonathan sun sa labule a fadar Aso Rock Villa

"Amma idan ba'a sakeshi a 2022 ba, kamar yadda shugabannin Arewa (Matasa ACF da Dattawan Arewa NEF) ke kira, babu zaben 2023 a gabashin Najeriya bisa ga dokar zaman gida da ake yi kuma hakan zai tsananta matsalar tsaro a kudancin Najeriya."

Ohaneaze Ndigbo
Idan Buhari na son zaman lafiya ya saki Nnamdi Kanu a shekarar nan, Ohaneaze Ndigbo
Asali: UGC

Buhari ya san muhimmancin sakin Nnamdi Kanu

Kungiyar ta bayyana cewa Shugaba Buhari ya san sakin Nnamdi Kanu zai taimaka wajen dawo da martabar Najeriya a idon duniya.

Hakazalika, Kabilar Igbo shirya take da mulkar Najeriya a 2023 don gyara kasar.

A cewar jawabin:

"Buhari ba zai iya kawar da kai daga sakin Nnamdi Kanu ba, zai taimaka wajen dawo da martabar Najeriya a idon duniya."
"A 2023 kuma, muna son shugaban kasa ya zama dan kablar Igbo saboda tabbatar da adalci da kuma biyayya ga yarjejeniyar da akayi na kama-kama a 1999."

Kara karanta wannan

Allah ya yiwa tsohon Shugaban Majalisar koli ta Shari'a, Dr Datti Ahmad, rasuwa

Asali: Legit.ng

Online view pixel