Yanzu-Yanzu: EFCC ta sanya gwamnan Anambra a jerin sunayen wadanda take nema

Yanzu-Yanzu: EFCC ta sanya gwamnan Anambra a jerin sunayen wadanda take nema

  • Gwamnan jihar Anambra ya shiga jerin mutanen da yaki da cin hanci da rashawa EFCC ke nema
  • Gwamna Willie Obiano shi ne gwamnan jihar Anambra mai barin gado watanni kadan masu zuwa
  • An ayyana sunan gwamnan ne a yau Laraba, amma har yanzu hukumar ta EFCC bata bayyana dalilin sanya sunansa ba

Anambra - Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta sanya Willie Obiano, gwamnan Anambra a cikin jerin sunayen wadanda take sa ido a kai.

Wannan batu ya zo ne watanni kafin Obiano ya bar ofis a matsayin gwamnan Anambra, kamar yadda TheCable ta ruwaito.

Gwamnan jihar Anambra, Willie Obiano
Yanzu-Yanzu: EFCC ta sanya gwamnan Anambra a jerin sunayen wadanda take nema | Hoto: thecable.ng
Asali: Facebook

A cewar wata wasika mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Nuwamba kuma zuwa ga kwanturola-janar na hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS), hukumar EFCC ta bukaci a sanar da ita duk lokacin da aka ga Obiano na yunkurin fita kasar waje.

Kara karanta wannan

Kotu ta daure jami’in gwamnatin tarayya a dalilin lakume miliyoyin kudin kwangila

Majiyoyi sun shaida wa Channels Tv cewa matakin wata alama ce da ke nuni da cewa hukumar ta yi bincike mai zurfi a kan gwamnan kuma ta yiwu ta samu bayanan sirri da ke nuna cewa yana shirin tserewa a ranar 16 ga Maris, 2022.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Gwamnonin da ke kan madafun iko a Najeriya na da kariya daga fuskantar tuhuma yayin da suke kan mulki.

Fani-Kayode ya yi magana bayan da EFCC ta kama shi kan jabun takardu

A wani labarin, Femi Fani-Kayode, tsohon ministan sufurin jiragen sama, ya musanta cewa hukumar EFCC ta kama shi.

Kakakin hukumar EFCC, Wilson Uwujaren, ya tabbatar da kama Fani-Kayode a yammacin ranar Talata, 23 ga watan Nuwamba, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

An ruwaito cewa an kama Fani-Kayode daga bisani aka kai shi ofishin hukumar ta EFCC na shiyyar Legas bisa zarginsa da yin magudi da kuma buga jabun takardu.

Kara karanta wannan

Da Duminsa: Fani-Kayode ya yi magana bayan da EFCC ta kama shi kan jabun takardu

Asali: Legit.ng

Online view pixel