Farashin mai na iya tashi N340 ga Lita a sabon shekara, GMD na NNPC

Farashin mai na iya tashi N340 ga Lita a sabon shekara, GMD na NNPC

  • An yi taron Bankin Duniya ranar Talata kuma maganganu sun yawaita kan lamarin tallafin man fetur
  • Masu ruwa da tsakin da suka halarci taron sun yi ittifakin cewa kawai a cire tallafin mai a 2022
  • Shugaban kamfanin NNPC ya bayyanawa yan Najeriya farashin da mai ka iya a sabuwar shekara

Dirakta Manaja na kamfanin NNPC, Malam Mele Kyari, ya tofa nasa albarkacin bakin kan lamarin cire tallafin man fetur a sabuwar shekarar 2022 da ake fuskanta.

A nasa jawabin, ya bayyana sabon farashin man da ake sa rai na iya konawa tsakanin N320 da N340 ga lita, rahoton Vanguard.

A cewarsa, da tun shekarar 2020 za'a cire tallafin amma wasu matsaloli suka taso kuma aka fasa hakan.

Yace amma daga 2022, doka ta wajabtawa gwamnati cire tallafin gaba daya.

Kara karanta wannan

Dukkan gwamnoni mun yarda Gwamnatin tarayya ta cire tallafin man fetur, Nasir El-Rufa'i

A cewarsa yanzu babu wani damar yin haka a doka, amma na san akwai wani aiki babba kan gwamnati na kula da talaka.

Kyari ya bada tabbacin cewa za'a cire tallafin a 2022 kuma farashin mai

Farashin mai na iya zama N340 ga Lita a sabon shekara, GMD na NNPC
Farashin mai na iya zama N340 ga Lita a sabon shekara, GMD na NNPC
Asali: Facebook

Zamu kara kudin mai, amma zamu fara baiwa yan Najeriya N5,000 kudin mota a wata: FG

Mun kawo muku cewa Ministar kudi, kasafin kudi da shirye-shiryen kasa, Zainab Ahmad Shamsuna, ta bayyana cewa Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari zata cire tallafin man fetur a 2022.

Idan Gwamnati ta cire wannan tallafi, kudin man fetur zai yi tashin gwauron zabo.

A madadin wannan tashi, Ministar kudin ta bayyana cewa Gwamnati za ta fara rabawa talakawan Najeriya dubu biyar-biyar a wata matsayin kudin mota.

Zainab ta bayyana hakan ne ranar Talata a taron kaddamar da rahoton Bankin Duniya (NDU).

Kara karanta wannan

Yanzu-yanzu: Zamu kara kudin mai, amma zamu fara baiwa yan Najeriya N5,000 kudin mota a wata: FG

A cewarta, talakawan dake Najeriya mutum guda milyan 30 zuwa 40 za'a rika baiwa wannan kudi wata-wata.

Tace amma sai an cire tallafin za'a san adadin yan Najeriya da zasu samu wannan kudi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel