Jerin sunaye da ma'aikatu: Matawalle ya ƙirƙiri sabbin ma'aikatu 4, ya sauya wa kwamishinoni wurin aiki

Jerin sunaye da ma'aikatu: Matawalle ya ƙirƙiri sabbin ma'aikatu 4, ya sauya wa kwamishinoni wurin aiki

  • Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya amince da kafa wasu ma’aikatu 4 na daban a jihar
  • Bayan kafa ma’aikatun ya kuma zabo sabon kwamishina ga ko wacce sabuwar ma’aikata
  • Ya kafa ma’aikatar kula da dajika da dabbobin kiwo, da ta samar da dukiya da ayyukan yi da sauran biyu

Jihar Zamfara - Gwamnan jihar Zamfara, Bello Matawalle ya tabbatar da samar da ma’aikatu 4 sannan ya zabo sababbin kwamishinoni na ma’aikatun.

Ya bayyana hakan ne ta wata takarda wacce sakataren gwamnatin jihar, Kabiru Balarabe ya bayyana a Gusau ranar Litinin bisa ruwayar The Punch.

Jerin sunaye da ma'aikatu: Matawalle ya ƙirƙiri sabbin ma'aikatu 4, ya sauya wa kwamishinoni wurin aiki
Gwamna Bello Matawalle na jihar Zamfara. Hoto: The Punch
Asali: Facebook

A cewar Balarabe, ma’aikatun da ya kafa guda 4 su ne:

Kara karanta wannan

Shekara daya da rabi da Shugaba Buhari ya yi magana, har yau umarninsa bai fara aiki ba

  • Ma’aikatar kula da dazuka da bunkasa kiwon dabobbi
  • Ma’aikatar samar da dukiya da kuma samar da ayyuka.
  • Ma’aikatar yawon bude ido da kula da otal da kuma
  • Ma’aikatar gina gidaje da bunkasa birane

Balarabe ya bayyana yadda gwamnatin ta nada sababbin kwamishinoni wadanda za su fara aiki daga nadin.

Ya lissafo ma’aikatun da kwamishinonin kamar haka;

  1. Ahmed Anka - Ma’aikatar ilimin kimiyya da fasaha
  2. Abubakar Dambo - Ma’aikatar harkokin kananun hukumomi
  3. Muh’d Magaji - Ma’aikatar al’adu
  4. Nasiru Masama - Ma’aikatar matasa da bunkasa wasanni
  5. Abdulaziz Nahuce - Ma’aikatar ayyuka na musamman
  6. Zainab Gummi - Ma’aikatar ilimi.
  7. Sufyan Yuguda - Ma’aikatar kudi
  8. Fa’eka Marshal - Ma’aikatar harkokin jin kai da annoba
  9. Rabiu Gusau - Ma’aikatar ayyuka da tafiye-tafiye
  10. Yazeed Fulani - Ma’aikatar sana’o’i da ma’aikatu
  11. Ibrahim Gusau - Ma’aikatar dazuka da bunkasa kiwon dabbobi
  12. Nuradden Gusau - Ma’aikatar ma’adanai
  13. Junaidu Kaira - Ma’aikatar shari’a
  14. Akwai Ibrahim Magayaki - Ma’aikatar noma
  15. Ibrahim Dosara - Ma’aikatar labarai
  16. Yahaya Gora - Ma’aikatar ilimin gaba da sakandare
  17. Yahaya Kanoma - Ma’aikatar samar da ayyuka da bunkasa arziki
  18. Lawal Badarawa - Ma’aikatar bunkasa al’umma
  19. Sheikh Jangebe - Ma’aikatar harkokin addini
  20. Aliyu Tukur - Ma’aikatar kasafi da tsari,
  21. Aliyu Tsafe - Ma’aikatar lafiya,
  22. Mamman Tsafe - Ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida,
  23. Abubakar Tsafe - Ma’aikatar yawon bude ido da kula da otal
  24. Ibrahim Mayana - Ma’aikatar ruwa
  25. Abubakar Bore - Ma’aikatar bunkasa kauyaku.

Asali: Legit.ng

Online view pixel