Tattalin arziki: Ngozi Okonjo-Iweala ta ba Ministocin Buhari muhimman shawarwari

Tattalin arziki: Ngozi Okonjo-Iweala ta ba Ministocin Buhari muhimman shawarwari

  • Dr. Ngozi Okonjo-Iweala tace yin kasuwanci yana da tsada sosai a Najeriya
  • Darektar WTO tayi kira ga gwamnati ta saukaka domin a bunkasa tattali
  • Okonjo-Iweala ta bayyana wannan ne da take jawabi wajen bitar Ministoci

Abuja - Darekta Janar na kungiyar kasuwanci na Duniya watau WTO, Dr. Ngozi Okonjo-Iweala, ta yi magana game da halin tattalin arzikin Najeriya.

Ngozi Okonjo-Iweala tace akwai bukatar Najeriya ta rage tsadar yin kasuwanci domin a kwadaito da masu hannun jari su zuba kudinsu a cikin kasar nan.

Jaridar Daily Trust tace Okonjo-Iweala tayi wannan magana a lokacin da tayi jawabi wajen taron bitar da aka shirya wa Ministocin tarayya a fadar Aso Villa.

Rahoton yace tsohuwar Ministar kudin tayi magana ne ta yanar gizo, ta ba Ministocin kasar shawarwarin da za su taimaka wajen inganta tattalin arziki.

Kara karanta wannan

Daukar aikin sojin sama: Abubuwa 14 da wadanda aka zaba suke bukatar tanada nan kusa

Dr. Okonjo-Iweala ta bayyana cewa dole a inganta tsaro idan ana so a jawo masu zuba hannun jari.

Ngozi Okonjo-Iweala
Dr. Ngozi Okonjo Iweala Hoto: www.ft.com
Asali: UGC

A jawabinta, masaniyar tattali da harkar kasuwancin tace tsadar kasuwanci a Najeriya, har ya zarce na sauran manyan kasashen wajen da suka cigaba.

Idan aka kamanta da sauran kasashen Afrika, kasuwanci a Najeriya ya fi tsada, sannan har yana nema ya zarce abin da ake kashe wa a kasashen Duniya.

Menene ya jawo wannan?

Baya ga haka, Okonjo-Iweala ta ce samar da abubuwan more rayuwa a Najeriya ya faye tsada, tace gwamnati da jami’an kwastam ne suka jawo wannnan.

Darektar ta WTO tace dakon kaya daga kamfani zuwa ga masu bukata yana cin kudi sosai a kasar nan.

Okonjo-Iweala tana ganin cunkoso da ake samu a tashohin kasar da tsadar dako suna cikin abubuwan da suka jawo kasuwanci yake da matukar wahala.

Kara karanta wannan

An yanke wa Salisu ɗaurin gidan yari kan satar tukwane da kujeru a coci a Legas

Miliyoyi za su rasa aikin yi

A ranar Asabar aka ji shugaban kungiyar masu kiwon kaji a Najeriya yana kuka game da yadda Dalar Amurka ta ke tashi, game da matsalar hatsi a Najeriya.

Kungiyar PAN tace mliyoyin mutane za su zama ba su da hanyar neman abinci idan aka yi sake. Ezekiel Ibrahim ya bayyana wannan da aka yi bikin ranar kwai.

Asali: Legit.ng

Online view pixel