An gano labarin matar da ta kashe ƴaƴanta 2 a Kano, da dalilin da ya sa ta kashe su

An gano labarin matar da ta kashe ƴaƴanta 2 a Kano, da dalilin da ya sa ta kashe su

- An gano labarin matar da ta kashe ƴaƴanta 2 a Kano

- Bayanai da aka tattara sun nuna cewa matar na da shafar aljanu

- Zuwa yanzu dai matar ta dage cewa lallai bata san abunda ya haddasa fada a tsakaninta da yaran ba ko kuma abunda ta aikata masu

Kamar yadda labari ya ta yaduwa a ranar Asabar, an zargi Hauwa’u Habibu da yi wa yaranta biyu yankan rago sannan ta tsere a gidanta da ke Kano.

Yayinda ake ta rade-radin cewa ta yi hakan ne saboda mijinta ya yi mata kishiya, jawabai sun nuna cewa ga dukkan alamu Hauwa’u na fama ne da matsala ta shafar aljanu.

Tuni dai yan sanda suka damke matar a kasa da sa’o’i 24 da afkuwar lamarin.

A binciken farko, wacce ake zargin ta fallasa cewa ta rufe gidansu, sannan ta yi amfani da adda da tabaryan karfe wajen far ma yaran su uku, inda ta ji masu munanan raunuka a sassan jikinsu.

Rundunar yan sandan sun kuma saki wasu faifan murya na hira da suka yi da wasu mutanen da lamarin ya shafa.

KU KARANTA KUMA: Ka daina zagin gwamnoninmu – PDP ta yi kakkausar gargadi ga shugaban rikon kwarya na APC

Babbar wacce ake zargi, Hauwa’u Habibu a hiran ta ce: “Abunda zan iya tunawa shine na ga mijina sanye da riga da ya jike da jini yana kai ni gidan iyayena, sannan ya bukaci da su ajiye ni a nan. Yawancin lokuta na kan ji wani irin yanayi a tattare dani sannan a yan kwanakin nan, na kan shiga yanayi na tsoro kuma na fada masa.”

Game da abunda ya wakana a wannan rana da abun ya afku, Hauwa’u ta ce: “Na gano yarana sun tunkaroni kamar muna fada. Sun tunkaroni da wani abu kamar wuka. Na fada ma mijina a baya cewa yana sauya mun zuwa halittu daban-daban. Wasu lokutan yana zuwa mun da kofato, dauke da abubuwa a jikinsa. Bai taba saurarata ba. Kawai dai na tafi gidan mahaifiyata, wacce itama ba son sabon aurensa take yi ba."

Ta dage cewa lallai bata san abunda ya haddasa fada a tsakaninta da yaran ba ko kuma abunda ta aikata masu.

“Sun biyoni da wuka. Kawai sai na tafi gidan mahaifiyata,” in ji ta.

Mijinta kuma uban yayanta, Ibrahim Haruna Aminu, ya ce: “Ta kira ni da safe da misalin karfe 9:55 tana fada mani cewa wasu mata biyu da namiji sun zo gidan za su kashe ta. Na tambayeta wanene a tare da ita da yaran sai ta fada mani cewa yaran ne za su kashe ta. Sai na fada mata ta ci gaba da addu’ a.

“Ana gobe abun zai faru tana ta abubuwa ba daidai ba. Na bukaci da ta ci gaba da addu’ a sannan cewa zan zo da zaran ruwan sama ya yi sauki. Bayan kimanin minti biyar, sai ta sake kira sannan ta mika wa yaran waya wadanda suka bukaci da na kawo masu abun sha na Bobo sai nace su je su dauki daddaya a dakina. Sai ta katse kiran.”

Ana haka, sai ya doshi gidan amma sai motarsa ta baci a hanya. Sai ya kira wani abokinsa wanda zai taya shi jan motar zuwa wajen bakaniki kafin ya tafi gida.

An gano labarin matar da ta kashe ƴaƴanta 2 a Kano, da dalilin da ya sa ta kashe su
An gano labarin matar da ta kashe ƴaƴanta 2 a Kano, da dalilin da ya sa ta kashe su Hoto: @daily_trust
Asali: Twitter

KU KARANTA KUMA: Ondo 2020: Dan Allah ka taka wa Akeredolu birki, PDP ta shawarci Buhari

“Da isana, sai na tafi gaishe da iyayena sannan na yi kokarin bude gidan wanda yake a rufe don haka sai nayi amfani da makullina. Da shigana gidan ne na ga gawawwakinsu,” in ji shi.

Wacce ta tsira a cikinsu, Aisha, ita ce ta fada mani cewa yayarta, Hauwa’u ce ta caccake su, sannan ta rufe gidan ta tafi.

“Sai na je gidanmu na fada ma yan uwana wadanda suka zo suka kwashi gawawwakin da wacce ta jikkata zuwa asibiti,” in ji shi.

Sannan sai ya tafi gidan surukansa inda ya tarar da matarshi tana hira da mahaifiyarta.

“Na fada mata abunda ya faru sai ta fashe da kuka sannan matata ta fara tambayar me ya faru,” in ji shi.

Mallam Adamu ya ce lallai matarsa bata cikin hayyacinta “saboda babu mutum mai hankali da zai aikata hakan ga yaransa.”

A bangaren mahaifiyarta ta ce 'yarta ta daɗe tana rashin lafiyar da ke da nasaba da iskokai.

Kakar yaran da aka kashe, Binta Ado Nababa ta, shaida wa BBC cewa yarta ta shafe tsawon wata uku ba ta iya bacci, "tana cewa kullum da dare ana zuwa ana danne ta ana shake ta. Ta fi wata uku ba ta bacci, da dare ana yi mata gurnani irin na dodanni."

"Da farko ban ɗauki maganarta da muhimmanci ba amma na faɗa mata cewa ta dinga yin addu'a kuma ta faɗa wa mijinta," in ji mahaifiyar matar.

Sai dai mahaifiyar ta ce tun da ta aurar da ƴarta shekara shida da suka gabata, yarta take tafka rikici da mijinta. "Kullum fada suke da mijinta," in ji ta.

Mahaifiyar ta ce ta taba zuwa neman kashe auren yarta saboda rikicin da kullum suke yi da mijinta.

"Saboda ita ta huta da rikicinta da mijinta. Wata daya da zuwa gidansa suke tafka rigima, kuma irin rikicin da suke yi ne har dangin mijin suke tunanin akwai abin da ke damunta," in ji ta.

Mahaifiyar ta kuma ce daga baya yarta ta samu rashin lafiyar, kuma yarta ta taba zuwa wurin malami har aka yi mata karatu amma rashin lafiyar ta kara tsanani.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel