Gwamnatin Najeriya ta ce Coronavirus ba ta gama kashe mutane ba tukuna

Gwamnatin Najeriya ta ce Coronavirus ba ta gama kashe mutane ba tukuna

Ministan harkokin kiwon lafiyan Najeriya, Osagie Ehanire, ya ce karuwar masu dauke da Coronavirus da ake samu a kasar nan, alama ce ta cewa za a samu karin mutanen da za su mutu.

Dr. Osagie Ehanire ya yi wannan gargadi ne a babban birnin tarayya Abuja kamar yadda jaridar Daily Trust ta bada rahoto a ranar Juma’a, 19 ga watan Yuni, 2020.

Da ya ke jawabi a lokacin da kwamitin shugaban kasa na yaki da cutar COVID-19 ta zanta da ‘yan jaridar, Miinistan ya ce sun dauki mataki na rage adadin wadanda cutar COVID-19 za ta kashe.

Ya ce: “Tun da mafi yawan wadanda su ke mutuwa, mutanen da su ka haura shekara 50 ne da haihuwa, ko kuma masu fama da wani rashin lafiya kamar ciwon sukari, kansa, hawan jini, ciwon koda, kanjamau da sauransu, rukunan wadannan mutane su na samun kariya ta musamman.”

“Shiga wuraren da za a samu cinkoso kamar kasuwa ko wuraren ibada ya na da hadari, haka zama a cikin killataccen daki ga mutum a kadaice, ya na kara barazanar kwayar cutar.”

KU KARANTA: Mutum kusan 800 aka samu dauke da COVID-19 a Ranar Alhamis

Gwamnatin Najeriya ta ce Coronavirus ba ta gama kashe mutane ba tukuna
Ministan lafiya a wurin taro
Asali: Twitter

A dalilin haka tsofaffi da masu larura bai kamata su killace kansu a daki musamman cikin dare ko a lokutan da babu kowa ba, domin cutar ta na iya bude mutum farat daya ba tare da an kawo agaji ba, inji Enahire.

Ministan ya kara da cewa: “Duk wanda gwaji ya nuna ya na dauke da cutar, ya kuma cigaba da zama a gida ko wani wuri, ayi maza a kai shi wurin jinya da zarar ya fara gaza numfashi.”

“Jinkiri ya na iya kawo babbar matsala, cutar ta na iya yin kamari a cikin lokacin da ba ayi tunani ba.” Ya ce: Wannan bakuwar cuta ta na cikinmu, ta na kama mutane kullum a cikin al’umma.”

Shugaban kula da wannan kwamiti na kasa, Dr. Sani Aliyu ya shaidawa jama’a cewa wannan annoba ba ta kama hanyar zuwa karshe ba, ya ce akwai karin yiwuwar mutane su kamu da cutar a yanzu.

Idan ku na da wata shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel