Jirgin sama dauke da fasinjoji fiye da 100 ya yi hatsari a Pakistan

Jirgin sama dauke da fasinjoji fiye da 100 ya yi hatsari a Pakistan

Rahotanni da ke zuwa mana sun nuna cewa wani jirgin sama dauke da fasinjoji 100 ya rikito a wani yanki a kasar Pakistan.

Hukumar kula da jiragen sama na kasar ta bayyana a ranar Juma’a, 22 ga watan Mayu, cewa jirgin ya rikito ne a birnin Karachi na Pakistan, Aljazeera ta ruwaito.

Abdul Sattar Khokhar, kakakin hukumar jirgin sama ta kasar, ya ce jirgin ya taso ne daga Lahore.

Jirgin sama dauke da fasinjoji fiye da 100 ya yi hatsari a Pakistan
Jirgin sama dauke da fasinjoji fiye da 100 ya yi hatsari a Pakistan Hoto: The News
Asali: UGC

Ya ce jirgin yana dauke da fasinjoji 99 da ma'aikatan jirgi takwas.

Hotunan da aka wallafa a shafukan intanet sun nuna hayaki ya turnuke sararin samaniya a wurin da jirgin ya fadi da ke rukunin gidaje da ke Karachi.

Ma'aikatan agajin gaggawa sun isa wurin da jirgin ya yi hatsari, inda ya lalata gidaje.

KU KARANTA KUMA: Gwamna Ayade ya zubar da hawaye yayinda ya dauke wa marasa karfi biyan haraji

A wani labari na daban, mun ji cewa a ranar Lahadi, 17 ga watan Mayu, 2020, gwamnatin tarayyar Najeriya ta bada sanarwar cewa ta tare jirgin sama na wani kamfani a kasar Birtaniya da ke aiki a sararin samaniyar kasar.

An kama jirgin ne ya na cigaba da daukar fasinjoji a daidai lokacin da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta haramta tashi da saukar duk wasu jiragen sama a fadin Najeriya.

Minista Hadi Sirika ya ce jirgin kamfanin Flair Aviation na kasar Birtaniya ne aka samu da laifin saba doka. Ba a ba wannan kamfani damar daukar fasinja ba inji ministan jiragen saman.

Mai girma ministan watau Hadi Sirika ya ce: “An ba wannan kamfani damar tashi domin zirga-zirgar taimakon jama’a ne, amma abin takaici sai mu ka kamu su, su na daukar fasinjoji.”

Da alamu cikin fushi, sanata Hadi Sirika ya fitar da jawabi: “Wannan rashin sanin ciwon kan sauran jama’a ne! An tsare jirgin saman, ana kuma yi wa ma’aikatan ciki tambayoyi.”

Bayan haka, Sirika ya rubuta cewa za a hukunta kamfanin a dalilin jawo fushin hukumomin kasar da ya yi a wannan marra. “Akwai hukunci mai matukar tsauri da ya ke jiransu”

Ministan harkokin jiragen saman na Najeriya ya bayyana wannan ne duk a shafinsa na Tuwita. Wannan sanarwa ta zo da kimanin karfe 2:30 na ranar yau Lahadi a agogon Najeriya.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel