Korona: Sabbin mutane 239 sun kamu a Najeriya; Bauchi, Kano da Katsina a sahun gaba

Korona: Sabbin mutane 239 sun kamu a Najeriya; Bauchi, Kano da Katsina a sahun gaba

Hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa a kasa (NCDC) ta ce annobar cutar covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 239 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11:20 na daren ranar Asabar, 09 ga watan Mayu, 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta sanar da cewa karin sabbin mutane 239 din sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

97-Lagos

44-Bauchi

29-Kano

19-Katsina

17-Borno

7-FCT

6-Kwara

5-Oyo

3-Kaduna

3-Sokoto

2-Adamawa

2-Kebbi

2-Plateau

2-Ogun

1-Ekiti

NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:20 na daren ranar Asabar, 09 ga watan Mayu, akwai jimillar mutane 4151 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a fadin Najeriya.

DUBA WANNAN: Bawa kudi fifiko ne yasa Buhari bai bawa Ganduje biliyoyin da ya nema domin yaki da korona ba - Fadar shugaban kasa

An sallami mutane 745 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 128.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel