Korona: Sabbin mutane 239 sun kamu a Najeriya; Bauchi, Kano da Katsina a sahun gaba

Korona: Sabbin mutane 239 sun kamu a Najeriya; Bauchi, Kano da Katsina a sahun gaba

Hukumar yaki da cututtuka ma su yaduwa a kasa (NCDC) ta ce annobar cutar covid-19 ta sake harbin sabbin mutane 239 a fadin Najeriya.

Hakan na kunshe ne a cikin sanarwar da NCDC ta fitar da misalin karfe 11:20 na daren ranar Asabar, 09 ga watan Mayu, 2020.

A cikin sanarwar da NCDC ta saba fitarwa a daren kowacce rana a shafinta na tuwita, ta sanar da cewa karin sabbin mutane 239 din sun fito daga jihohin Najeriya kamar haka;

97-Lagos

44-Bauchi

29-Kano

19-Katsina

17-Borno

7-FCT

6-Kwara

5-Oyo

3-Kaduna

3-Sokoto

2-Adamawa

2-Kebbi

2-Plateau

2-Ogun

1-Ekiti

NCDC ta ce ya zuwa karfe 11:20 na daren ranar Asabar, 09 ga watan Mayu, akwai jimillar mutane 4151 da aka tabbatar da cewa suna dauke da kwayar cutar covid-19 a fadin Najeriya.

DUBA WANNAN: Bawa kudi fifiko ne yasa Buhari bai bawa Ganduje biliyoyin da ya nema domin yaki da korona ba - Fadar shugaban kasa

An sallami mutane 745 bayan an tabbatar da sun warke sarai, a yayin da cutar ta hallaka jimillar mutane 128.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng