Yadda takalma suka tona wa wasu 'yan fashi da makami asiri a Zaria

Yadda takalma suka tona wa wasu 'yan fashi da makami asiri a Zaria

Wani shaida mai suna Sajan Jamilu Tanimu da ke aiki da ofishin ‘yan sanda a Zaria, ya labarta yadda takalman da aka bari a wajen da aka yi fashi da makami suka tona asrin ‘yan fashin.

Tanimu yaa bayyana hakan ne a jiya Alhamis yayin da yake bada shaida a gaban wata kotun majistare da ke Zaria, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Dan sanda mai gabatar da karar, Sajan Yau Garba, ya fara gabatar da karar ne a ranar 20 ga watan Fabrairun 2020. Wadanda ake karar kuwa masu suna Isah Abdullahi da Mubarak Abdullahi dukkansu masu shekaru 17 ne daga anguwan Dan Madami a birnin Zaria.

Mai gabatarwar ya ce wadanda ake karar ana zarginsu ne da hada kai wajen aikata laifi, balle gida da kuma tsoratarwa wanda hakan ya ci karo da sassa na 58, 327, 377, 270 da 332 na dokokin Penal Code na jihar Kaduna.

Shaidar ya sanar da kotun cewa, a ranar 6 ga watan Fabrairu wajen karfe 10:30 na dare sun fasa gida, sun yi sata tare da tsorata wanda yayi kara mai suna Alhaji Yahaya Sani.

Yadda takalma suka tona wa wasu 'yan fashi da makami asiri a Zaria
Yadda takalma suka tona wa wasu 'yan fashi da makami asiri a Zaria
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: Ganduje ya bayar da umurnin rufe dukkan makarantun Kano saboda Coronavirus

Tanimu ya ce mai karar ya bayyana yadda ‘yan fashi suka shiga mishi gida tare da kwashe musu kayayyaki amma sai suka bar takalmansu.

Bayan kwanaki tara kuwa sai aka kama Isah na sata a wani gida da ke kusa da na wanda ya kai korafin. “A yayin bincike, Isah ya bayyana cewa tare suke da Mubarak. Amma kuma daga baya sai suka musanta zargin da ake musu,” yace.

Bayan tsananta bincike ne aka gano cewa wadannan takalman mallakin Mubarak ne. Amma kuma har yanzu ba a kama komai ba daga cikin abinda aka sata a hannunsu.

Hakazalika, shaidar ya kasa yin bayanin yadda takalman suka kai gidan mai korafin.

Alkali Ruqayyat Ummi Ahmed ta dage sauraron shari’ar zuwa ranar 26 ga watan Maris don ba wa mai gabatar karar kawo shaidarsa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel