Gwamnan Bauchi ya yi umurnin kama tsoffin gwamnoni Yuguda da Abubakar tare da hukunta su

Gwamnan Bauchi ya yi umurnin kama tsoffin gwamnoni Yuguda da Abubakar tare da hukunta su

- Gwamnan jahar Bauchi, Bala Mohammad ya yi umurni kama tsoffin gwamnonin jahar guda biyu

- Tsoffin gwamnnin sune Isa Yuguda da MA Abubakar wadanda ake zargi da sace kadarorin gwamnatin jahar na triliyoyin nairori a lokacin da suke kujerar mulki

- Hakan ya biyo bayan karban rahoton kungiyar dawo da kadarorin jahar da aka sace

Gwamnan jahar Bauchi, Bala Mohammad ya yi umurni kamawa da hukunta tsoffin gwamnoni Isa Yuguda da MA Abubakar wadanda ake zargi da sace kadarorin gwamnatin jahar na triliyoyin nairori a lokacin da suke kujerar mulki.

Gwamnan ya bayar da umurnin ne lokacin da ya samu rahoton kwamitin kwato kadarorin jahar da aka nada a ranar 12 ga watan Yuli, 2019 sannan aka umurce su da su binciki zargin karkatar da kadarori a tsakanin 2007 da 2019 a zauren majalisa, gidan gwamnatin Bauchi.

Gwamnan Bauchi ya yi umurnin kama tsoffin gwamnoni Yuguda da Abubakar tare da hukunta su
Gwamnan Bauchi ya yi umurnin kama tsoffin gwamnoni Yuguda da Abubakar tare da hukunta su
Asali: UGC

Gwamna Bala wanda ya ce lallai dole jami’an gwamnati su kasance da bayanan abubuwa dalla-dalla ya sha alwashin dawo da arzikin jahar da kuma tabbatar da hukunta tsoffin gwmnonin da jami’ansu da kwamitin ya samu da laifi.

Ya ce atoni janar na jahar da wasu mambobin kwamitin Za su hadu su yi nazari a kan shawarwarin da kwamitin dawo da dukiyoyin suka bayar don hukunta wadanda ke da hannu a ciki.

KU KARANTA KUMA: Mafakar Sanusi: Gwamnan Nasarawa ya kira taron gaggawa na manyan sarakuna

Mukaddashin shugaban kwamitin, Ritaya Janar Markus Koko Yake yayinda yake gabatar da rahoton ga gwamnan ya ce kwamitin ta gano badakala daban daban da kuma karkatar da kadarorin gwamnati daga ma’aikatu, da hukumomi 19 takanin 2007 da 2019 lokacin da Yuguda da Mista Abubakar suka yi shugabanci a matsayin gwamnonin jahar.

An tattaro cewa kwamitin ya bukaci tsoffin gwamnonin da sauransu da su dawo da kudaden da ake zargin sun sata a lokacin mulkinsu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel