Zamfara: Kotu ta tsare tsohon kwamishinan Yari da aka gurfanar da laifin satar Shanu da garkuwa da mutane

Zamfara: Kotu ta tsare tsohon kwamishinan Yari da aka gurfanar da laifin satar Shanu da garkuwa da mutane

A ranar Juma'a ne wata babbar kotun Sharia da ke zamanta a Gusau, jihar Zafara, ta bayar da umarnin a tsare tsohon kwamishinan kananan hukumomin jihar Zamfara, Bello Dankande, bayan an gurfanar da shi a gabanta bisa zarginsa da hannu a satar Shanu da garkuwa da Mutane.

Jaridar TheCable ta rawaito cewa umarnin da kotu ta bayar a kan Danakande yana zuwa ne a cikin kasa da sa'a 48 da wata kotun jihar ta bayar da umarnin tsare wani jigo a jam'iyyar APC a jihar Zamfara.

Kotun ta bayar da umarnin tsare sakataren yada labarai a kwamitin jam'iyyar APC bayan an gurfanar da shi a gabanta bisa tuhumarsa da laifin ingiza jama'a da bata suna.

An gurfanar da Dankande ne a gaban kotun mai shari'a, Jastis Hadi Sani, bisa zarginsa da yin garkuwa da wasu mutane biyu da kuma samunsa da hannu a satar Shanu 50 da Tumaki 50.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng