Ganduje Vs Sanusi: Gwamnatin Kano ta biya sarki Sanusi II diyar N4.5m bayan ta rushe filinsa na N250m

Ganduje Vs Sanusi: Gwamnatin Kano ta biya sarki Sanusi II diyar N4.5m bayan ta rushe filinsa na N250m

Gwamnatin jihar Kano ta kwace tare da rushe wani filin sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, da darajarsa ta kai miliyan N250, sannan ta amince da biyansa miliyan N4.5 kacal a matsayin kudin diyya.

Akwai 'yan rigingimu a tsakanin gwamnan jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da sarki Sanusi II, lamarin da yasa gwamnatin Kano a karkashin jagorancin gwamna Ganduje ta kirkiri sabbin masarautu hudu domin rage wa basaraken karfi.

A cikin satin da ya gabata ne wata babbar kotu a Kano a karkashin mai shari'a Usman Na'abba ta soke dokar da ta bawa gwamnatin jihar damar kirkirar sabbin sarakunan yanka 4 masu daraja daya da sarki Sanusi II.

Sai dai, wasu masu nazarin al'amura sun bayyana cewa hukuncin kotun kan iya lalata sauran 'yar kyakyawar alakar da ta rage a tsakanin jagororin biyu.

Wani binciken hadin gwuiwa da jaridun 'Daily Nigerian' da 'Kano Focus' suka gudanar a kan filin da aka rushe, sun gano cewa filin yana kan titin Ibrahim Dabo a cikin birnin Kano kuma an rushe shi ne domin gina gada a shataletalen shagon sayar da maguguna na 'Dangi'.

Jaridun sun bayyana cewa kwamishinan aiyuka, Injiniya Muaz Magaji, shine da kansa ya jagoranci rushe filin a ranar Juma'a, 15 ga watan Nuwamba, 2015.

Wasu ma'aikatan hukumar kasa da safayo a jihar Kano sun sanar da jaridun cewa sarki Sanusi ya sayi filin mai girman hekta 1.2 a shekarar 2010 a kan kudi miliyan N200, tare da bayyana cewa darajar filin yanzu ta kai miliyan N250m.

Da aka tuntubi shugaban ma'aikatan fadar sarkin Kano, Munir Sanusi, a kan batun ya ce ba zai iya cewa komai a kai ba saboda sarki Sanusi bai bashi damar yin magana a kan lamarin ba.

Sai dai, wata majiya a cikin fadar Kano ta sanar da cewa har yanzu gwamnatin Kano bata biya Sarki Sanusi II ko sisi ba matsayin diyya.

A hirar da wakilan jaridun suka yi da kwamishinan aiyukan, ya yi ikirarin cewa gwamnatin jihar Kano ta biya Sarki Sanusi diyyar kudin filin da aikin hanyar ya shafa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel