An yi wa wata yarinya bulala 80 da laifin shan tabar wiwi a jihar Kaduna
Wata kotun shari'ar musulunci da ke zamanta a unguwar Magajin Gari ta jihar Kaduna, ta yanke wa wata budurwa masi shekaru 19 a duniya, Zainab Abdullahi, hukuncin bulala 80 biyo bayan kama ta da laifin shan tabar wiwi a bainar al'umma.
Da yake zartar da hukuncinsa a ranar Alhamis, Alkalin kotun Malam Muhammad Shehu Adamu, ya zartar da wannan hukunci a kan Zainab bayan ta amsa laifin da ake zarginta da aikata wa na shan tabar wiwi a filin Allah.
A rahoton da jaridar The Punch ta ruwaito, Alkali Shehu ya ce bulala 80 shi ne hukuncin da shari'a tayi tanadi ga duk wanda aka akama da laifi makamancin wanda Zainab ta aikata na shaye-shayen kayan maye.
Ya gargadi kungiyar musulmi ta Najeriya, MCN, a kan ta ci gaba ayyuka na gari da ta saba kuma tayi kokari wajen ladabtar da Zainab domin koma wa hanyar gaskiya.
KARANTA KUMA: Bamu taba kawo wa Buhari zai yi nasara ba a kotun sauraron karar zabe - Bitrus Porgu
Jami'i mai shigar da kara a gaban kotu, Ibrahim Shu'aibu, ya bayar da shaidar cewa jami'an tsaro na 'yan sanda ne suka cafke Zainab a yayin da take tsaka da zukar tabar wiwi a kan titi.
Kamar yadda Shu'aibu ya bayyana a gaban kotu, an taba kama Zainab da laifi kuma tayi zaman gidan Dan Kande a sanadiyar gaza biyan kudin tara na N7,000 da aka shimfida a kanta har zuwa lokacin da kungiyar MCN ta fito da ita bayan ta biya tarar da ke rataye a wuyanta.
Sanarwa: Mun gode da kasancewarku tare damu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa
Domin shawara ko bukatar ba mu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:
https://facebook.com/legitnghausa
https://twitter.com/legitnghausa
Asali: Legit.ng