An cafke matashin da ya cilla jariri cikin ruwa a jihar Neja

An cafke matashin da ya cilla jariri cikin ruwa a jihar Neja

Hukumar jami'an tsaron cikin gida ta Najeriya NSCDC, a ranar Talata 10 ga watan Satumban 2019, ta cafke wani matashin dan acaba mai shekaru 20 kacal a duniya, Aliyu, da laifin cilla jaririnsa dan watanni hudu da haihuwa a cikin rafi.

Kwamadan hukumar NSCDC reshen jihar Neja, Mr George Edem, shi ne ya bayar da tabbacin wannan mummunan rahoto da cewar wanda ake zargi ya aikata laifin ne a kauyen Tamanine na karamar hukumar Borgu a jihar.

An tattaro cewa, ya zuwa yanzu ba a gano gawar jaririn ba duk da binciken da jami'ai suka dukufa wajen gudanarwa kamar yadda jaridar The Punch ta ruwaito.

Mr Edem ya ce za a mika Aliyu a hannun hukumar 'yan sanda domin ci gaba da binciken wannan lamari da rataya a wuyanta.

A nasa bangaren, Aliyu ya ce ya jefar da jaririn ne a bayan ya yi sukuwa a kan dokin zuciya sanadiyar yadda mahaifiyarsa da kuma mahaifiyar budurwarsa suka dora masa karan tsana tun bayan haihuwarsa watanni kadan da suka gabata.

KARANTA KUMA: Buhari ya kebance da shugaban Red Cross a fadar Villa

Ya ce bakin cikin yadda mahaifiyarsa a kullum take barazanar tsinewa jaririn da kuma buduwarsa wadda a kullum take cikin zubar hawaye a sanadiyar yadda mahaifiyarta ta kyamaci jaririn, ya sanya ya yanke wannan danyen hukunci.

A yayin da ya ke nadamar wannan mummunar ta'asa da ya aikata, Aliyu ya ce a shirye yake domin fuskantar duk wani hukunci da doka tayi tanadi.

Sanarwa: Mun gode da kasancewarku tare damu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar ba mu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo mu a shafukan mu na dandalin sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng