Gwamna Ganduje yayi sabbin nade-nade masu muhimmanci a gwamnatinsa

Gwamna Ganduje yayi sabbin nade-nade masu muhimmanci a gwamnatinsa

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na jihar Kano ya amince da nadi da sake nadin wasu shugabannin hukumomin gwamnati a jihar.

Babban sakataren labaran gwamnan, Malam Abba Anwar ne ya sanar da hakan a wani jawabi da ya saki a ranar Talata, 16 ga watan Yuli a Kano.

Daga cikin wadanda aka nada sun hada da Sheikh Abdalla Pakistan a matsayin Shugaban hukumar kula da jin dadin mahajattan jihar Kano da kuma Dr Aliyu Musa a matsayin Darakta-Janar na hukumar Hisbah a jihar.

Anwar ya bayyana cwa an nada Dr Halima Rabi’u Abdullah a matsayin babbar sakatariyar hukumar ilimi da kuma Alhaji Gali Sadiq a matsayin Manajan Darakta na kamfanin Radiyo na jihar Kano.

A cewarsa, gwamnan ya kuma sake nada Dr Ibrahim Bichi a matsayin babban sakataren dakin karatu na jihar Kano da kuma Sagir Sadisu Buhari a matsayin Darakta-Janar na hukumar bincike.

An kuma sake nada Lawan Sabo a matsayi n Manajan-Darakta na kamfanin buge-bugen takardu, Sa’a Ibrahim Manajan Darakta na Abubakar Rimi Television (ARTV), Dr Hibrilla Mohammed Manajan Darakta na KSIP.

KU KARANTA KUMA: Buhari ma babban dan adawar Obasanjo ne a baya – Shehu Sani ya waiwayi tarihi

Sauran sun hada da Alhaji Ibrahim Galadima, Shugaban kungiyar wasanni na Kano da kumaMista Sakina Yusuf a matsayin Shugaban kotun kula da harkokin Hajji na jihar Kano.

Gwamnan ya yaba ma wadanda aka sake ba mukami kan isar da ayyukansu da suka yi da kyau a mulkinsa na farko sannan yayi kida da dukkanin wadanda aka ba mukamai das u ci gaba da sauke hakkokin da ke kansu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng