Majalisar dokokin jihar Kaduna ta tabbatar da kwamishinoni 11

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta tabbatar da kwamishinoni 11

Majalisar dokokin jihar Kaduna a ranar Alhamis, 4 ga watan Yuli ta tabbatar da mutane 11 wadanda gwamna Nasir El-Rufai ya gabatar a matsayin kwamishinoni a jihar.

Daga cikin wadanda aka tabbatar akwai kakakin gwamnan, Samuel Aruwan a matsayin kwamishinan tsaron cikin gida da harkokin gida.

Yan majalisar sun fara tabbatar da Mohammed Bashir Saidu wanda ya kasance tsohon kwamishinan kudi da shugaban ma’aikata ga gwamnan jihar a gwamnatin da ya gabata.

Ba da bata lokaci ba Yan majalisar suka bukaci yayi biyayya ya tafi saboda yayi ma jihar hidima a mukamai da dama a cewar kakakin majalisa Aminu Shagali.

Mutum na biyu da aka tabbatar shine Jafaru Ibrahim Sani daga karamar hukumar Kubau wanda ya kasance tsohon kwamishinan ilimin na jihar a gwamnatin da ya gabata. Shi ma yayi biyayya ba tare da tambayoyi ba.

An tantance Hafsat Mohammed Baba a matsayin kwamishinar ma’aikatar ayyuka da cigaba inda majalisar ta bukace ta da tayi biyayya ta tafi, kamar yanda aka bukaci Samuel Aruwan wanda yayi bauta a matsayin babban hadimin gwamna kan kafofin yada labarai da sadarwa wanda a halin yanzu an tabbatar da shi a matsayin kwamishinan tsaron gida da harkokin gida.

KU KARANTA KUMA: Ana shirin kai wadanda suka daura aure a Facebook kotu a Kano

Sauran kwamishinonin da aka tabbatar sun hada da Mohammed Shehu Usman Makarfi wanda ya kasance sakatare na dindindin a ma’aikatar kiwon lafiya a matsayin kwamishinan ilimi.

Idris Samaila Nyan na ma’aikatar kasuwanci, kirkire-kirkiren fasaha da Ibrahim Garba Hussaini a Ma’aikatar muhalli da albakatu.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari, Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aisha Musa avatar

Aisha Musa (Hausa writer) Aisha Musa 'yar jarida ce wacce ta kwashe shekaru biyar tana aikin gogewa a harkar yada labarai. Ta kammala karatun ta a Jami'ar Ibrahim Badamasi Babangida (IBB Lapai) a shekarar 2014 tare da digirin farko a fannin Tarihi. Aisha Editan Hausa ce wacce ke amfani da kwarewa da kwazonta don karfafawa wasu gwiwar yin aiki tukuru don cimma nasara. Ta karbi lambar yabo na gwarzuwar shekarar 2021 a bangaren Hausa na Legit. Za ku iya aika mata sakonnin imel ta adireshinta aisha.musa@corp.legit.ng