Sabon gwamnan Nasarawa ya yi wasu muhimman sabbin nade-nade

Sabon gwamnan Nasarawa ya yi wasu muhimman sabbin nade-nade

Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasararwa ya yi nade-naden a karo na farko bayan darewarsa kan mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2019.

Sanarwar nadin mukamen na dauke ne cikin sakon da sakataren harkokin mulki na ofishin sakataren gwamnatin jihar, Abubakar Ishaq ya fitar a ranar Asabar a garin Lafia.

Ishaq ya ce gwamnan ya amince da nadin manyan masu bawa gwamna shawara na musamman guda tara da za su fara aiki daga ranar 1 ga watan Yuni.

DUBA WANNAN: Zanga-zanga: Jami'an tsaro sun shiga farautar mabiya Shi'a a Abuja

Wadanda aka yiwa nadin sun hada da John Mamman, Mai bayar da shawara kan harkokin sarauta; Samuel Egya, Mai bayar da shawara na ofishin gwamna; Yakubu Kwanta, Mai bayar da shawara kan harkokin matasa da kungiyoyi masu zaman kansu; da Murtala Lamus, Mai bayar da shawara kan ayyuka na musamman.

Saura sun hada da Ibrahim Abdullahi, Mai bayar da shawara kan saka hannun jari da tsarin tattalin arziki; James Thomas, Jami'in sadarwa na Abuja; Rakiya Alaku, Mai bayar da shawara kan harkokin mata da bayar da tallafi; Salihu Ogah, Ofishin mataimakin gwamna da Abubakar Zanwa, Mai bayar da shawara kan harkokin shari'a.

Ishaq ya kuma bayyana cewa gwamnan yana son a rika kiransa da Abdullahi A. Sule.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku Latsa: Domin karuwa cikin wannan wata mai albarka na Ramadana

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164