Sabon gwamnan Nasarawa ya yi wasu muhimman sabbin nade-nade

Sabon gwamnan Nasarawa ya yi wasu muhimman sabbin nade-nade

Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasararwa ya yi nade-naden a karo na farko bayan darewarsa kan mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2019.

Sanarwar nadin mukamen na dauke ne cikin sakon da sakataren harkokin mulki na ofishin sakataren gwamnatin jihar, Abubakar Ishaq ya fitar a ranar Asabar a garin Lafia.

Ishaq ya ce gwamnan ya amince da nadin manyan masu bawa gwamna shawara na musamman guda tara da za su fara aiki daga ranar 1 ga watan Yuni.

DUBA WANNAN: Zanga-zanga: Jami'an tsaro sun shiga farautar mabiya Shi'a a Abuja

Wadanda aka yiwa nadin sun hada da John Mamman, Mai bayar da shawara kan harkokin sarauta; Samuel Egya, Mai bayar da shawara na ofishin gwamna; Yakubu Kwanta, Mai bayar da shawara kan harkokin matasa da kungiyoyi masu zaman kansu; da Murtala Lamus, Mai bayar da shawara kan ayyuka na musamman.

Saura sun hada da Ibrahim Abdullahi, Mai bayar da shawara kan saka hannun jari da tsarin tattalin arziki; James Thomas, Jami'in sadarwa na Abuja; Rakiya Alaku, Mai bayar da shawara kan harkokin mata da bayar da tallafi; Salihu Ogah, Ofishin mataimakin gwamna da Abubakar Zanwa, Mai bayar da shawara kan harkokin shari'a.

Ishaq ya kuma bayyana cewa gwamnan yana son a rika kiransa da Abdullahi A. Sule.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Ku Latsa: Domin karuwa cikin wannan wata mai albarka na Ramadana

Asali: Legit.ng

Online view pixel