Buhari ya bawa shugabannin hukumomin tsaro umarnin gaggawa a kan kisan jihar Katsina

Buhari ya bawa shugabannin hukumomin tsaro umarnin gaggawa a kan kisan jihar Katsina

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bawa babban sifeton rundnunar 'yan sanda (IGP), Mohammed Abubakar Adamu, da babban hafsan rundunar sojojin Najeriya (COAS), Janaral Abayomi Gabriel Olonisakin, umarnin kafa kwamitin da zai binciko abinda ya faru a jihar Katsina tare da mika masa rahoto cikin gaggawa.

A sanarwar da Bashir Ahmad, mai taimaka wa shugaban kasa a bangaren kafafen sadarwa na zamani, ya fitar a shafinsa na Tuwita ya ce shugaba Buhari ya bukaci shugabannin hukumomin tsaron da su binciko yadda aka kaddamar da hare-hare a kan wasu al'ummomi a jihar Katsina duk da kasancewar ana cikin watan Ramadana mai alfarma.

Kazalika ya umarci su dauki matakan da zasu tabbatar da hakan bata sak faruwa ba a nan gaba.

A ranar Talata ne Legit.ng ta kawo muku labarin cewar wasu 'yan bindiga sun kashe fiye da mutane 26 a wani hari da suka kai a kan mazauna wasu garuruwa dake kananan hukumomin Dan Musa, Faskari da Batsari dake jihar Katsina.

Majiyar mu ta sanar da mu cewar 'yan bindigar sun kai harin ne ranar Talata a kan babura.

Buhari ya bawa shugabannin hukumomin tsaro umarnin gaggawa a kan kisan jihar Katsina
Buhari da shugabannin hukumomin tsaro
Asali: Facebook

A cewar majiyar, an kashe mutane 11 a garin Sabon Layin Galadima dake karkashin karamar hukumar Faskari, yayin da aka kashe mutane biyar a Mara Zamfarawa dake karamar hukumar Dan Musa tare da sace dabbobi da dama.

Gidan Talabijin na Channel ya rawaito cewar 'yan bindigar sun kai wa wasu manoma hari a gonakin su a kauyen 'Yar Gamji dake karamar hukumar Batsari, inda suka kashe mutane 18, yayin da aka rasa mutane 10.

Kakakin rundunar 'yan sandan jihar Katsina, SP Gambo Isah, ya ce wadanda aka kashe a karamar hukumar Faskari mambobin kungiyar bijilanti ne.

DUBA WANNAN: 'Yan sanda sun harbe Shaho; shugaban gungun masu garkuwa da mutane a hanyar Abuja

A cewar sa, "wasu 'Yansakai a kauyen Sabon Layi a karamar hukumar Faskari sun bi 'yan bindigar cikin daji tun jiya amma har yanzu basu dawo ba. Mazauna kauyen sun samu nasarar gano gawar mutum biyu daga cikin su kuma tuni sun binne su.

"Mun tura runduna 'yan sanda karkashin jagorancin DPO din Faskari domin nemo ragowar kuma su ma sun yi nasarar gano karin gawar mutane uku. Kazalika mun gano wani sansani da 'yan ta'addar suka taba amfani da shi. Muna cigaba da gudanar da bincike," a cewar DSP Isah.

A dangane da harin Dan Musa da Batsari, DSP Isah ya ce rundunar 'yan sanda tana kokarin samun karin bayanai.

"Muna kokarin samun rahotanni har yanzu," a cewar sa.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Domin sauke manhajar labaran Legit.ng a wayar ku ta hannu, latsa wannan rubutu na kasa:

https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.android&pid=solomonovlink

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng