Jerin ministocin Buhari, sunaye, ma'aikatu da kuma jihohin su
Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Laraba, 22 ga watan mayun 2019, ya jagoranci zaman majalisar zantwar na bankwana yayin da rage saura sati daya a rantsar da shi a kan wani sabon wa'adi na jagorancin kasar nan karo na biyu.
A yau ne shugaban kasa Buhari zai karkare zaman majalisar zantarwa na mako-mako da aka ska saba gudanar wa a fadar sa ta Villa da ke garin Abuja.
Majalisar zantarwa ta Najeriya ta kunshi shugaban kasa, mataimakin sa, Ministoci, shugaban ma'aikatan gwamnati na baki daya da kuma shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasa.
KARANTA KUMA: Hukumar jiragen sama ta kasa NCAA ta shiga yajin aiki na sai baba ta gani
Ana ci gaba da cece-kucen cewa akwai yiwuwar shugaban kasa Buhari zai sallami dukkanin Ministoci bayan kammala zaman majalisar zantarwa na bankwana domin samun damar nadin sabbi da za su rike madafan iko a wa'adin gwamnatin sa na biyu.
Tiryan Tiryan ga jerin Ministocin shugaba Buhari, sunaye, ma'aikatu da kuma jihohin da suka fito a fadin Najeriya kamar haka:
1. Ministan Labarai da Al'adu; Alhaji Lai Muhammad (Jihar Kwara)
2. Ministan Kwadado; Chris Ngige (Anmabra)
3. Ministan Sufuri; Rotimi Amaechi (Ribas)
4. Ministan Makamashi, Ayyuka da Gidaje; Babatunde Fashola (Legas)
5. Ministan harkokin cikin gida; Abdulrahman Dambazau (Kano)
6. Ministan Kimiya da Fasaha; Ogbonaya Onu (Ebonyi)
7. Ministan Shari'a kuma Lauyan Kolu na kasa; Abubakar Malami (Kebbi)
8. Ministan Sufurin jiragen Sama; Hadi Sirika (Katsina)
9. Ministan Sadarwa; Adebayo Shittu (Oyo)
10. Ministan Ruwa; Suleiman Adamu (Jigawa)
11. Ministan Matasa da wasanni; Solomon Dalong (Filato)
12. Ministan Man Fetur; Ibe Kachikwu (Delta)
13. Karanin Ministan Lafiya; Dakta Osagie Ehanire (Edo)
14. Ministan Noma; Audu Ogbeh (Benuwai)
15. Ministan kasafi da tanadin kasa; Udo Udo Udoma (Akwa Ibom)
16. Karamin Ministan Zamantakewa; Ibrahim Usman Jibril (Nasarawa)
17. Ministan Neja Delta; Claudius Omoyele Daramola (Ondo)
18. Ministan Ilimi; Anthony Onwuka (Imo)
19. Ministan harkokin kasashen ketare; Geoffery Onyeama (Enugu)
20. Ministan Tsaro; Masur Dan Ali (Zamfara)
21. Ministan Kudi; Zainba Ahmed (Kaduna)
22. Ministan masana'antu da hannun jari; Okechukwu Enelamah (Abia)
23. Ministan Birnin Tarayya; Muhammad Bello (Adamawa)
24. Ministan Makamashi; Mustapha Baba Shehuri (Borno)
25. Ministan Harkokin Mata; Aisha Abubakar (Sakkwato)
26. Karamin Ministan Noma; Heineken Lokpobiri (Bayelsa)
27. Ministan Ilimi; Adamu Adamu (Bauchi)
28. Ministan Lafiya; Isaac Adewole (Osun)
29. Ministan Neja Delta; Usani Uguru (Kuros Riba)
30. Karamin Ministan Ma'adanan kasa; Abubakar Bawa Bwari (Neja)
31. Ministan Zamantakewa; Suleiman Hassan (Nasarawa)
Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.android&pid=solomonovlink
Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Ku biyo cikin shafukan mu na dandalan sada zumunta a Facebook ko kuma Twitter:
https://facebook.com/legitnghausa
https://twitter.com/legitnghausa
Ku fa'idantu da manhajar mu ta Azumi a wannan wata mai albarka a wannan shafi:
https://fb.gg/play/ramadan_ramadan
Asali: Legit.ng