Abinda ya sa kasashen da suka cigaba basa son taimakon Najeriya - Buhari
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce wasu daga cikin kasashen da suka cigaba basa son taimakon Najeriya ne saboda kuskuren tunanin cewar Najeriya kasa ce mai arziki.
A cewar jawabin da Garba Shehu, kakakin shugaban kasa, ya fitar a ranar Alhamis, shugaba Buhari ya fadi hakan ne yayin karbar takardun fara aiki na jakadun kasashe uku da suka hada da Indiya, Kuwait da Namibia a Abuja.
Shugaba Buhari ya fada wa jakadan kasar Kuwait, Al Bisher, cewar, "an kwakuba Najeriya cikin kasashen duniya masu arzikin man fetur, ta zama mamba a kungiyar kasashen duniya masu sayar da danyen man fetur a kasuwar duniya (OPEC).
"Sannan goyon bayan wasu daga cikin manufofin kasashen kungiyar OPEC, a wasu lokutan, ya na hana kasashen da suka cigaba taimakon Najeriya bisa kuskuren tunanin cewar Najeriya kasa ce mai arziki." a cewar jawabin.
DUBA WANNAN: Kotu ta tsige Sanatan APC, ta ce dole ya biya albashi da alawus din da ya karba cikin mako 2
Sannan ya kara da cewa "Najeriya za tayi murna da taimako a bangaren ilimi, fasaha, da aiyukan raya kasa da za su inganta rayuwar jama'a."
A martanin sa, Al Bisher ya kasar Kuwait ba ta saka Najeriya cikin kasashen Afrika da ta ke yiwa aiyukan raya kasa ba a karkashin shirin 'Kuwait Project' da suka kirkira a kasashen Afrika a shekarar 1961. Ya kara da cewa amma yanzu za a saka Najeriya cikin jerin kasashen.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng