Abinda ya sa kasashen da suka cigaba basa son taimakon Najeriya - Buhari

Abinda ya sa kasashen da suka cigaba basa son taimakon Najeriya - Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce wasu daga cikin kasashen da suka cigaba basa son taimakon Najeriya ne saboda kuskuren tunanin cewar Najeriya kasa ce mai arziki.

A cewar jawabin da Garba Shehu, kakakin shugaban kasa, ya fitar a ranar Alhamis, shugaba Buhari ya fadi hakan ne yayin karbar takardun fara aiki na jakadun kasashe uku da suka hada da Indiya, Kuwait da Namibia a Abuja.

Shugaba Buhari ya fada wa jakadan kasar Kuwait, Al Bisher, cewar, "an kwakuba Najeriya cikin kasashen duniya masu arzikin man fetur, ta zama mamba a kungiyar kasashen duniya masu sayar da danyen man fetur a kasuwar duniya (OPEC).

Abinda ya sa kasashen da suka cigaba basa son taimakon Najeriya - Buhari
Buhari
Asali: Facebook

"Sannan goyon bayan wasu daga cikin manufofin kasashen kungiyar OPEC, a wasu lokutan, ya na hana kasashen da suka cigaba taimakon Najeriya bisa kuskuren tunanin cewar Najeriya kasa ce mai arziki." a cewar jawabin.

DUBA WANNAN: Kotu ta tsige Sanatan APC, ta ce dole ya biya albashi da alawus din da ya karba cikin mako 2

Sannan ya kara da cewa "Najeriya za tayi murna da taimako a bangaren ilimi, fasaha, da aiyukan raya kasa da za su inganta rayuwar jama'a."

A martanin sa, Al Bisher ya kasar Kuwait ba ta saka Najeriya cikin kasashen Afrika da ta ke yiwa aiyukan raya kasa ba a karkashin shirin 'Kuwait Project' da suka kirkira a kasashen Afrika a shekarar 1961. Ya kara da cewa amma yanzu za a saka Najeriya cikin jerin kasashen.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng