Takaitacen tarihin Marigayi Justice Mamman Nasir
An haifi Jastis Nasir a shekarar 1929 a jihar Katsina. Ya yi karatun makarantar sakandire a Kaduna, inda ya samu takardar shaidar kammala karatun sakandire ta kasashen yammacin Afrika (WAEC) a shekarar 1947.
Marigayin ya halarci jami'ar Ibadan kafin daga bisani ya wuce kasar Ingila, inda ya kammala karatunsa na digiri a bangaren shari'a a shekarar 1956.
Bayan dawowarsa Najeriya a shekarar 1956, an nada shi a matsayin alkali kafin daga bisani a nada shi a matsayin minista shari'a, na yankin arewacin Najeriya, a shekarar 1961, mukamin da ya rike na tsawon shekaru biyar.
DUBA WANNAN: Shugabancin majalisa: Lawan ya bijrewa umurnin Oshiomhole, ya nemi goyon bayan 'yan PDP
A shekarar 1967 ne aka nada shi a matsayin darektan sashen gurfanarwa na yankin arewa kafin daga bisani ya zama mai kula da shari'a a yankin arewa ta tsakiya, mukamin da ya rike har zuwa lokacin da aka nada shi a matsayin daya daga cikin alkalan kotun koli a shekarar 1975.
A shekarar 1978 ne aka nada shi a matsayin shugaban kotunan daukaka kara na Najeriya, mukamin da ya rike har zuwa lokacin da ya yi ritaya a shekarar 1992,shekarar da aka nada shi a matsayin Galadiman masarautar Katsina.
Ya kuma rasu ranar Asabar 13 ga watan Afrilun 2019.
Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/legitnghausa
Twitter: https://twitter.com/legitnghausa
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Asali: Legit.ng