Takarar shugaban kasa: Nine zabin Shehu Yar'Adua tun 1993 - Atiku

Takarar shugaban kasa: Nine zabin Shehu Yar'Adua tun 1993 - Atiku

- Dan takarar shugabancin kasa na PDP, Atiku Abubakar ya fadawa Katsinawa cewa marigayi Shehu Yar'Adua ya zabe shi a matsayin shugabancin Najeriya tun 1993

- Atiku Abubakar ya roki Katsinawa su taimaka masa domin ganin wannan mafarkin na marigayi Yar'Adua ta zama gaskiya

- Ya yi alkawarin kawar da yunwa da fatara daga Najeriya tare da dawo da martabar kasar a idanun kasashen duniya idan an zabe shi

A ranar Alhamis ne dan takarar shugabancin kasa na jam'iyyar PDP a zaben ranar 16 ga watan Fabrairu, Atiku Abubakar ya ce marigayi Janar Shehu Musa Yar'Adua ya zabi shi domin zaman shugaban kasar Najeriya tun a 1993.

Takarar shugaban kasa: Nine zabin Shehu Yar'Adua tun 1993 - Atiku
Takarar shugaban kasa: Nine zabin Shehu Yar'Adua tun 1993 - Atiku
Asali: UGC

DUBA WANNAN: Hotunan yadda kaddamar da yakin neman zaben Buhari ta kasance a Adamawa

Atiku ya yi wannan ikirarin ne a yayin da ya ke jawabi da taron jiga-jigai da magoya bayansa a yayin kaddamar da yakin neman zabensa a Karakanda Stadium da ke jihar Katsina.

A jawabin da dan takarar shugaban kasar ya yi cikin harshen hausa, ya ce, "Marigayi Shehu Yar'Adua ya zabe ni a matsayin shugaban kasar Najeriya tun a 1993. Yanayin siyasar Najeriya ce ta hana hakan afkuwa.

"Ina kira a gare ku Katsinawa ku tallafa min domin ganin mafarkin Yar'Adua ya zama gaskiya. Ku zabe n domin in kawar da yunwa da fatara daga Najeriya. Ku zabi Yaku Lado a matsayin gwamna domin jihar mu ta Katsina da samun cigaban da gwamnatin APC ta gaza samarwa."

Tsohon gwamnan jihar Katsina, Shehu Shema da ya yi jawabi a wurin taron shima ya yi kira ga masu zabe su kada kuri'arsu ga 'yan takarar jam'iyyar PDP.

Ya ce, "Alhaji Atiku Abubakar shine mutumin da zai iya mulkin Najeriya a yanzu. Lokaci ya yi da zamu zabi mutumin da ke kwarewa ya kuma hada kan Najeriya. Atiku shine wanda zai iya gudanar da wannan aikin.

"Idan kuka zabe shi a matsayin shugaban kasa, zai kawar da yunwa da fatara daga Najeriya, zai kuma tabbatar Najeriya ta dawo da mutunci da martabar ta idanun kasashen duniya."

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164