Cikin Hotuna: Atiku ya gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara

Cikin Hotuna: Atiku ya gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara

A yau Litinin 4 ga watan Fabrairu, dan takarar kujerar shugaban kasa na jam'iyyar adawa ta PDP, Atiku Abubakar, ya girgiza magoya bayan sa yayin taron yakin neman zabe da ya gudanar cikin birnin Gusau na jihar Zamfara da ke Arewa maso Yammacin Najeriya.

Yayin ci gaba da yawon shawagi da karade jihohi 36 domin neman goyon bayan al'umma sakamakon kusantowar babban zaben kasa, a yau Litinin, Atiku ya girgiza magoya bayan sa a jihar Zamfara.

Atiku yayin dirar sa a birnin Shehu gabanin zuwan sa jihar Zamfara
Atiku yayin dirar sa a birnin Shehu gabanin zuwan sa jihar Zamfara
Asali: Twitter

Shugaban jam'iyyar PDP na kasa Prince Uche Secondus cikin raha da manyan magoya baya
Shugaban jam'iyyar PDP na kasa Prince Uche Secondus cikin raha da manyan magoya baya
Asali: Twitter

Atiku yayin musabaha da jiga-jigan PDP a Birnin Shehu
Atiku yayin musabaha da jiga-jigan PDP a Birnin Shehu
Asali: Twitter

Atiku yayin isowar Kwankwaso harabar taron yakin zabe a jihar Zamfara
Atiku yayin isowar Kwankwaso harabar taron yakin zabe a jihar Zamfara
Asali: Twitter

Kwankwaso yayin jaddada akidar PDP a taron yakin zabe na jihar Zamfara
Kwankwaso yayin jaddada akidar PDP a taron yakin zabe na jihar Zamfara
Asali: Twitter

Atiku yayin girgiza magoya baya a jihar Zamfara
Atiku yayin girgiza magoya baya a jihar Zamfara
Asali: Twitter

Shugaban jam'iyyar PDP na kasa tare da dan takarar kujerar gwamnan jihar Zamfara
Shugaban jam'iyyar PDP na kasa tare da dan takarar kujerar gwamnan jihar Zamfara
Asali: Twitter

Al'umma sun karbi akida ta goyon bayan Atiku yayin gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara
Al'umma sun karbi akida ta goyon bayan Atiku yayin gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara
Asali: Twitter

Al'umma sun karbi akida ta goyon bayan Atiku yayin gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara
Al'umma sun karbi akida ta goyon bayan Atiku yayin gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara
Asali: Twitter

Al'umma sun karbi akida ta goyon bayan Atiku yayin gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara
Al'umma sun karbi akida ta goyon bayan Atiku yayin gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara
Asali: Twitter

Atiku yayin gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara
Atiku yayin gudanar da taron yakin neman zabe a jihar Zamfara
Asali: Twitter

Kwankwaso yayin taron yakin neman zaben PDP a jihar Zamfara
Kwankwaso yayin taron yakin neman zaben PDP a jihar Zamfara
Asali: Twitter

Jaridar Legit.ng ta ruwaito cewa, tsohon gwamna kuma wakilin shiyyar Kano ta Tsakiya a majlisar dattawa, Sanata Rabi'u Musa Kwankaso, ya halarci taron yakin neman zaben Atiku da aka gudanar da misalin karfe 10.00 na safiyar yau cikin birnin Gusau.

Cikin jawaban sa da ya zayyana, Atiku ya sha alwashin inganta harkokin tsaro a jihar Zamfara tare da habaka harkokin kasuwanci a yayin da ya cimma nasara ta kasancewa jagoran al'ummar Najeriya baki daya.

KARANTA KUMA: Tsaro: El Rufa'i zai yiwa sarakunan gargajiya ihsani a jihar Kaduna

Jaridar Legit.ng ta fahimci cewa, furucin tsohon mataimakin shugaban kasar na inganta harkokin ya sosawa al'ummar Zamfara wurin da ya ke masu ciwo sakamakon yadda suke ci gaba da fuskantar barazanar ta'addanci ba ga birni ko kauyukan su ba.

Kazalika jaridar ta ruwaito cewa, Wazirin ya gudanar da taron yakin neman zaben sa a jiya Lahadi cikin Birnin Kebbi inda ya girgiza magoya baya na al'umma da suka cika kuma suka batse domin nuna tsagwaran soyayyar su.

Sanarwa: Ku ci gaba da kasancewa tare da mu yayin da Shafin Naij.com Hausa ya sauya suna zuwa Legit.ng Hausa

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayarku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa

Domin shawara ko bukatar bamu labari, tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Ku biyo cikin shafukan mu na zaurukan sada zumunta:

https://facebook.com/legitnghausa

https://twitter.com/legitnghausa

Asali: Legit.ng

Online view pixel