Yadda musulmi da Kirista zasu zauna lafiya da juna - Sultan
- Yakamata musulmi da kirista so zauna lafiya
- Shuwagabannin addinai suna da damar sanya fahimtar juna a tsakanin mutane masu mabambantan addini
- Ya bayyana bacin ransa akan yanda akayi watsi da lamarin tarihi a bangaren zabarshi a bangaren karatu

Asali: Twitter
A ranar Litinin Sultan din Sokoto Sa'ad Abubakar ||| ya shawarci malaman addini dasu kirkiro wasu dabaru da zasu samar da zaman lafiya tsakanin musulmai da kiristoci.
Mr Abubakar ya bayyana haka ne a wani taro da jami'ar jihar Nassarawa ta hada.
Yace shuwagabannin addinai suna da damar kawo wasu abubuwa da zasu sanya a samu karin fahimtar juna a tsakanin masu banbancin addinai.
Sa'ad Abubakar ya wakilci sarkin jihar Keffi Shehu Yamusa ||| a wajen taron.
DUBA WANNAN: Za'a baiwa Ro-Safti makamai
Sannan ya kara da bayyana bacin ransa akan yanda akayi watsi da karantar zabar bangaren tarihi a kasar nan.
A yayin da Vice Chancellor na jami'ar yake tofa albarkacin bakin sa yace " rashin kyakkyawan Shugabanci shine ya janyo talauci da rashin tsaro".
Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng
Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng