Kasar Faransa zata dawo da ababen tarihi da ta kwasa daga nahiyar Afirka
- Kasar Faransa zata dawowa da Jahuriyar Benin kayan tarihin ta
- Kasar Faransa ta kwace kayan ne a wani yaki da akayi a shekara ta 1892
- A shekara ta 2016 Benin ta nemi Faransa data dawo mata da kayayyakin ta.

Asali: Twitter
A ranar Juma'a ne shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya amince da maidawa jamhuriyar Benin kayan tarihin ta ba tare da wani jinkiri ba.

Asali: Facebook
Wannan batu zai sanya tsofaffin masu mulkin mallaka a matsin lamba akan kasashen Afurika kayan su da aka kwace.
Macron ya amince zai maida ababan tarihi 26 wanda ya hada da gumaka,kasar Faransa ta kwace wadannan kayane a lokacin wani yaki a shekara ta 1892.
DUBA WANNAN: Ko kun kula, Jonathan bayyi zancen kudin makaman Dasuki a littafin sa ba sam-sam?
A shekara ta 2016 Benin ta nemi Faransa data dawo mata da Ababan tarihin ta wanda ya hada da gumaka,zanuka da kuma abubuwan da ta sassaka.
Wanda a wancan lokacin shugaban kasar yaki amincewa da wannan bukata a watan Nuwamba na shekara ta 2016.
Sanarwa: Shafin Naij.com Hausa shine yanzu ya koma Legit.ng Hausa, don inganta muku zafafan labarai dama kayatarwa
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng
Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng