Idan mu ka kira Ambode a waya don mu taimake sa a APC ba ya dauka - Adefuye
Labari ya iso mana cewa Anthony Adefuye wanda yana cikin manyan Jam’iyyar APC a Jihar Legas ya bayyana irin kokarin da su kayi na sasanta Gwamna Akinwumi Ambode da kuma Asiwaju Bola Tinubu.
Anthony Adefuye wanda daya ne daga cikin Majalisar GAC masu ba Gwamna shawara a Legas yace yayi bakin kokari wajen dinke barakar da ta shigo Jam’iyyar APC mai mulki a Jihar wanda tayi sanadiyyar Gwamna Ambode ya rasa tikiti.
Adefuye yace sun nemi su ga Gwamna Akinwumi Ambode ya samu tikitin tazarce a APC, akasin abin da mutane ke rayawa na cewa sun hana sa zarcewa. Jigon Jam’iyyar yace sun nemi su gana da Gwamnan a lokacin amma abin ya faskara.
Babban ‘Dan siyasar yace duk kokarin da su kayi na saduwa da Gwamna Ambode a lokacin ana tsakiyar rikicin zabe ya ci tura. Adefuye yace sun dade da hango cewa Ambode zai samu matsala a zaben APC don haka su ka nemi a dauki mataki.
KU KARANTA: Duk da na fadi amma zan yi kokarin ganin Buhari ya zarce inji Ambode
Mista Adefuye yace ko da su ka kira Gwamna Ambode a waya domin su nuna masa inda baraka ta ke, sai su ka ga ba ya daukar wayan su. Adefuye yace sun nemi Mataimakin Shugaban kasa Osinbajo ya sa baki a rikicin Gwamnan da Tinubu.
Anthony Adefuye yace ya tashi tare da wani babban ‘Dan APC a Legas Alhaji Tajudeen Olusi su ka samu Tinubu domin jin abin da yake faruwa a lokacin tsakanin sa da Gwamna Ambode amma sai su ka ji dai Gwamnan shi ma bai daukar wayan sa.
A karshe dai bayan duk sun yi abin da za su iya dole aka saduda inji Jigon na APC. Adefuye yace ana ji ana gani Gwamna mai-ci Akinwunmi Ambode ya sha kasa Babajide Sanwo-Olu wajen wanda Bola Tinubu ya tsaida.
Idan ka na da wata shawara ko bukatar ba mu labari, a tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng
Ku same mu a https://www.facebook.com/legitnghausa
Ko a http://twitter.com/legitnghausa
Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta LEGIT NG Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Shafin NAIJ Hausa ya koma LEGIT
Asali: Legit.ng