'Yan kasuwa sun yiwa El-Rufai ihu, sunyi watsi da tayin da ya yi musu

'Yan kasuwa sun yiwa El-Rufai ihu, sunyi watsi da tayin da ya yi musu

Wani abin mamaki ya faru a kasuwar Sheikh Abubakar Gumi da ke Kaduna inda 'yan kasuwar suka gwale gwamna Nasir El-Rufai na jihar bayan ya yi alakwarin sake gina musu shagunansu da gobara ta afkawa.

Rahottani sun bayyana cewar El-Rufai ya kai ziyarar bazata ne a kasuwar a ranar Talata bayan ya samu labarin cewar Sanata Shehu Sani mai wakiltan mazbar Kaduna ta Tsakiya ya ziyarci kasuwar a ranar Litinin.

An ruwaito cewar 'yan kasuwar sun katsewa gwamna El-Rufai hanzari yayin da ya ke jawabi inda suka rika kasa ihu suna cewa: "Bama so, Bama so, Shakaru hudu kawai za kayi."

Yan kasuwanni sun gwale El-Ruai kan rokonsu da yayi wai zai sake gina musu shagunansu
Yan kasuwanni sun gwale El-Ruai kan rokonsu da yayi wai zai sake gina musu shagunansu
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: El-Rufai ya canjawa wani babban sarki a Kaduna suna bayan ya mayar da shi sarkin yanka

Shehu Sani ya kai ziyara kasuwar ne a ranar Litinin misalin karfe 11 na safiya domin ganawa da mutanen yankinsa kuma sun karbe shi hannu biyu-biyu inda suka rika yabonsa kan yadda ya ke kusantar talakawa da kuma ayyukan da ya keyi a majalisa.

Sani ya bayar da gudunmawa na N1 miliyan ga wadanda gobara ta kone shagunansu da ke kusa da layin dogo a kasuwar kuma ya dauki alkawarin daukan nauyin karatun yaran 'yan kasuwan da suka rasu har na tsawon shekaru biyu.

A kwana-kwanan nan ne a Abuja, El-Rufai ya kallubalanci Sani da ya shiga cikin kasuwar ta Abubakar Gumi ya gani ko zai fito lafiya domin a cewar El-Rufai yan kasuwar suna fushi da shi sai dai Sani ya shiga kuma ya fita lafiya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Authors:
Aminu Ibrahim avatar

Aminu Ibrahim (Hausa HOD) Aminu Ibrahim leads the Hausa Desk at Legit.ng. He holds a Bachelor's degree in Microbiology from Ahmadu Bello University, Zaria, and pursued further with a Master's degree in Environmental Microbiology from Federal University Dutse, Jigawa. With over seven years of experience, Aminu has honed his craft in news reporting and content editing, weaving narratives that captivate and inspire audiences: aminu.ibrahim@corp.legit.ng or +2348030996164