'Yan kasuwa sun yiwa El-Rufai ihu, sunyi watsi da tayin da ya yi musu

'Yan kasuwa sun yiwa El-Rufai ihu, sunyi watsi da tayin da ya yi musu

Wani abin mamaki ya faru a kasuwar Sheikh Abubakar Gumi da ke Kaduna inda 'yan kasuwar suka gwale gwamna Nasir El-Rufai na jihar bayan ya yi alakwarin sake gina musu shagunansu da gobara ta afkawa.

Rahottani sun bayyana cewar El-Rufai ya kai ziyarar bazata ne a kasuwar a ranar Talata bayan ya samu labarin cewar Sanata Shehu Sani mai wakiltan mazbar Kaduna ta Tsakiya ya ziyarci kasuwar a ranar Litinin.

An ruwaito cewar 'yan kasuwar sun katsewa gwamna El-Rufai hanzari yayin da ya ke jawabi inda suka rika kasa ihu suna cewa: "Bama so, Bama so, Shakaru hudu kawai za kayi."

Yan kasuwanni sun gwale El-Ruai kan rokonsu da yayi wai zai sake gina musu shagunansu
Yan kasuwanni sun gwale El-Ruai kan rokonsu da yayi wai zai sake gina musu shagunansu
Asali: Twitter

DUBA WANNAN: El-Rufai ya canjawa wani babban sarki a Kaduna suna bayan ya mayar da shi sarkin yanka

Shehu Sani ya kai ziyara kasuwar ne a ranar Litinin misalin karfe 11 na safiya domin ganawa da mutanen yankinsa kuma sun karbe shi hannu biyu-biyu inda suka rika yabonsa kan yadda ya ke kusantar talakawa da kuma ayyukan da ya keyi a majalisa.

Sani ya bayar da gudunmawa na N1 miliyan ga wadanda gobara ta kone shagunansu da ke kusa da layin dogo a kasuwar kuma ya dauki alkawarin daukan nauyin karatun yaran 'yan kasuwan da suka rasu har na tsawon shekaru biyu.

A kwana-kwanan nan ne a Abuja, El-Rufai ya kallubalanci Sani da ya shiga cikin kasuwar ta Abubakar Gumi ya gani ko zai fito lafiya domin a cewar El-Rufai yan kasuwar suna fushi da shi sai dai Sani ya shiga kuma ya fita lafiya.

Muhimmiyar sanarwa: Shafin NAIJ.com Hausa ya koma LEGIT.ng Hausa. Mun gode da kasancewarku tare da mu.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: : https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/legitnghausa

Twitter: https://twitter.com/legitnghausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel