Manyan ayyukan cigaba guda 4 da jahar Zamfara ta amfana dasu daga gwamnatin tarayya
A yayin da kakar zaben shekarar 2019 ke kara kartowa, yan siyasa na cigaba da kokarin ganin kodai sun zarce a kujerun da suka yi dare dare akai, ko kuma kokarin ganin dan gidansu ko kuma duk wanda suka tsayar takara ya kai labari.
Haka zalika wasu yan siyasan na tuna ma jama’ansu alkawurran da suka yi musu kuma suka cika musu, domin da haka ne kadai jama’a masu zabe zasu auna kokarin da dan siyasan ya yi, sai su yanke hukuncin cancantarsa ko akasin haka.
KU KARANTA: Take hakkokin bil adama: Majalisar dinkin Duniya ta fara binciken kasashe 14, har da Najeriya
Da wannan ne Legit.com ta binciko wasu manyan ayyukan cigaba da gwamnatin tarayya a karkashin jagorancin shugaban kasa Muhammadu Buhari wanda ya dare mukamin bayan samun nasara a zaben shekarar 2015.

Asali: Facebook
An sha mamaki a yayin wannan zabe dai, inda dan adawa Buhari ya kayar da shugaba mai ci, shugaban kasa Goodluck Jonathan, inda Buhari ya samu kuri’u sama da miliyan goma sha biyar yayin da Jonathan ya samu kuri’u miliyan goma sha biyu da yan kai.
Al’ummar jahar Zamafar ma ba’a barsu a baya ba wajen kada ma Buhari kuri’u, inda bayan kammala zaben hukumar zabe mai zaman kanta, INEC, ta sanar da Buhari ya samu kuri’u dubu dari shida da goma sha biyu, da dari biyu da biyu (612, 202).
A sakamakon gudunmuwar da jama’an jahar suka baiwa Buhari, babu yadda za’ayi ya manta dasu, don haka ga wasu daga cikin muhimman ayyukan cigaba da Buharin ya yi a Zamfara:
- Aikin gina babbar hanyar Kasuwar Daji-Gusau
- Aikin gina gidaje don amfanin jama’a
- Daukan matasa 32, 186 a karkashin tsarin N-Power
- Aikin tabbatar da tsaro na operation sharan daji
Ku biyo mu a https://facebook.com/legitnghausa
ko a http://twitter.com/legitcomhausa
Ga masu shawara ko korafi, a same mu a labaranhausa@corp.legit.com
Sanarwa na musamman: Shafin NAIJ Hausa ya koma Legit Hausa
Asali: Legit.ng