Kabilanci: Kaduna ta zama kasasshiyar jiha karkashin El-Rufain APC - Hunkuyi

Kabilanci: Kaduna ta zama kasasshiyar jiha karkashin El-Rufain APC - Hunkuyi

- Anyi kashe-kashe tsakanin kabilun jihar Kaduna

- An dade ana qiyayya ga juna, kuma babu alamun sassautawa

- Sanata Hunkuyi ya koka

Kabilanci: Kaduna ta zama kasasshiyar jiha karkashin El-Rufain APC - Hunkuyi
Kabilanci: Kaduna ta zama kasasshiyar jiha karkashin El-Rufain APC - Hunkuyi
Asali: Depositphotos

Sanatan PDP, mai wakiltar Kaduna ta arewa, ya koka da yawan tashe-tashen hankula da ake samu a Kaduna da kewaye, saboda bambancin kabila, da addini.

A cewarsa, jihar ta ffadi warwas a jarrabawar zaman laffiya, karkashin mulkin APC, da Malam Nasuru Rufai.

Ya kuma yi kira da a fito da basarake da yake zaman garkuwa, hannun mutane da har yanzu ba'a san ko su waye ba, basaraken dai Sarkin Kabilar Adara ne.

DUBA WANNAN: Wadanda Saudiyya ta kashe a shekarun nan

An sanya dokar ta baci a jihar, inda aka takaita zirga-zirga da ma baza jami'ai a lunguna da sakoki na jihar.

Babu dai ranar da kasar nan zata zauna lafiya, tunda kabilunta sun kasa zama lafiya da juna, manya da qanana, kowa ya tsani kowa, na bangaren kabila daban, na bangaren addini daban.

Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng

Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com

Asali: Legit.ng

Authors:
Mudathir Ishaq avatar

Mudathir Ishaq Mudathir Ishaq is the head of the Hausa desk at Legit.ng. He studied Industrial Chemistry as first degree at the University of Abuja, Journalism (CSR Specialization) with the Michigan State University and runs MSc Industrial Chemistry from the Nasarawa State University, Keffi. With more than a decade experience in news reporting and content editing, he has interviewed influential personalities. He can be reached on: mudathir.ishaq@corp.legit.ng