Zaku ga karshen ta'addanci nan ba da jimawa ba - Buhari
- Shugaban kasa Muhammadu Buhari yayi alkawarin kawo karshen ta'addanci a kasar nan
- Ya yabawa yan Nageriya bisa goyan baya da suke basu da kuma addu'o'i
- Fatan mu shine mu kasance cikin kwanciyar hankali da walwala

Asali: Facebook
A ranar Juma'a shugaban kasa Muhammad Buhari ya jaddada kudirin sa na kawo karshen ta'addacin da rigingimu a fadin kasar nan.
Da yake maganar a kungiyar Tijjaniya Shura yace gwamnatin zataci gaba da sanya ido akan harkar ta'addanci da kuma tattalin arziki,tare da fatan samun nasara.
Shugaban ya yabawa yan Nageriya bisa goyan baya da suke basu da kuma gudummawar addo'o'in su .
"naji dadi matuka da addu'o'in ku da kuma goyan baya da kuke bamu" ya fada.ya zama dole mu zage dantse dan kawowa kasar tamu cigaba.
DUBA WANNAN: An kama dan acaba da laifin ganganci a titi
A nasa furucin shugaban tijjaniyya Sheikh Ibrahim Maihula yace" fatan mu shine mu rayu a kasar da take da kwanciyar hankali da kuma tattalin arziki,sannan zamuci gaba dayi muku addu'a tare da duk wani magoyin bayanka.
Latsa wannan domin samun labarai a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en
Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:
Facebook: https://facebook.com/hausa.legit.ng
Twitter: https://twitter.com/hausa.legit.ng
Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,
Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.com
Asali: Legit.ng