Dakarun sojin sun kara yiwa mayakan kungiyar Boko Haram 23 raga-raga, duba hotunan makaman da aka samu

Dakarun sojin sun kara yiwa mayakan kungiyar Boko Haram 23 raga-raga, duba hotunan makaman da aka samu

A jiya, Talata, 11 ga watan Yuni, dakarun sojin Najeriya tare da hadin gwuiwar sojojin jamhuriyar Kamaru suka yiwa wasu mayakan kungiyar Boko Haram kaca-kaca tare da kwato wasu makaman da kayan da mayakan ke amfani da su.

Daga cikin makaman da dakarun sojin suka yi nasarar kwatowa daga hannun mayakan akwai bindigu kirar AK 47 guda 6, wasu Karin bindigu 2 samfurin FN, alburusai masu yawa da kwanson su da kuma Babura guda 2.

Sojin sun yi nasarar kasha mayakan kungiyar ta Boko Haram guda 23 tare da raunata wasu da dama.

Dakarun sojin sun kara yiwa mayakan kungiyar Boko Haram 23 raga-raga, duba hotunan makaman da aka samu
Wasu daga cikin bindun da aka kwato

Dakarun sojin sun kara yiwa mayakan kungiyar Boko Haram 23 raga-raga, duba hotunan makaman da aka samu
Motar mayakan kungiyar Boko Haram da aka yiwa raga-raga

Dakarun sojin sun kara yiwa mayakan kungiyar Boko Haram 23 raga-raga, duba hotunan makaman da aka samu
Bindigu da Baburan mayakan kungiyar Boko Haram

Kafin wannan arangama, dakarun sojin sun yi nasarar kakkabe ragowar mayakan kungiyar Boko Haram daga maboyar su a kauyukan dake makwabtaka da tekun Chadi da suka hada da; Bulakeisa, Tumbuma Babba, Abbaganaram, Dan Baure da sauran su.

DUBA WANNAN: Ki taimake ni, ke ma fa kirista ce - Karanta yadda gwamna Dariye ya yi ruwan magiya ga alkaliya bayan yanke masa hukunci

Hukumar soji, tab akin darektan yada labarai, Texas Chukwu, ta shawarci jama’ar jihar Borno da suke gaggauta sanar da jami’an tsaro duk wani motsin mutane da basu yarda das hi domin daukan mataki a kan lokaci.

Latsa wannan domin samun sabuwar manhajar labarai ta Legit.ng Hausa a wayar ku ta hannu: https://play.google.com/store/apps/details?id=com.naij.hausa&hl=en

Ku biyo mu a shafukanmu na dandalin sada zumunta:

Facebook: https://facebook.com/naijcomhausa

Twitter: https://twitter.com/naijcomhausa

Idan kuna da wata shawara ko bukatar bamu labari,

Tuntube mu a: labaranhausa@corp.legit.ng

Asali: Legit.ng

Online view pixel