Jihar Zamfara
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci kan matafiya a jihar Zamfara. Tsagerun sun sace fasinjoji tare da kashe direban motar.
Kungiyar matasan Yarabawa (YYC), ta bi sahun masu kiran da a sanya dokar ta baci a jihar Zamfara. Sun ce hakan zai sanya a samu zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Yayin da rashin tsaro ke sake taɓarɓarewa a Zamfara, Kungiyar NDYC ta bukaci gwamnatin tarayya ta ayyana dokar ta baci a jihar saboda yawaitar kashe-kashe.
'Yan bindiga dauke da makamai sun kai hare-haren ta'addanci a juhar Zamfara. Miyagun wadanda suka kai hare-haren a wasu kauyuka uku, sun hallaka mutane 28.
Wasu miyagun 'yan bindiga dauke da bindiga sun kai hare-hare a jihar Zamfara. 'Yan bindigan sun kashe jami'in tsaro tare da yin awon gaba da mutane masu yawa.
Bayan tone-tone da Gwamna Dauda Lawal ya yi kan basuka, tsohon kwamishinan yada labarai, Ibrahim Dosara, ya musanta ikirarin cewa ya samu N4m kacal.
Yan bindiga sun tilasta wa ƙauyuka 12 da ke karamar hukumar Maru a jihar Zamfara biyan harajin N60m bisa zargin ba sojoji bayanai da ke kawo musu tarnaki.
Yayin da ake ta jita-jitar Gwamnan Zamfara zai bar PDP, Dauda Lawal ya fito ya ƙaryata labarin inda ya ce har yanzu shi cikakken dan jam'iyyar ne ba makawa.
Wasu majiyoyi sun tabbatar da cewa rundunar dojoji sun yi kwanton bauna inda suka hallaka Ibrahim Kaboni da wasu ‘yan bindiga takwas a garin Tsafe da ke Zamfara.
Jihar Zamfara
Samu kari