Jihar Zamfara
Marigayi Dr Ibrahim Bello ya shafe shekara 10 a kan mulki bayan zama Sarkin Gusau a 2015. Ya rike mukamai da dama ciki har da aikin koyarwa kafin sarauta.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal Dare ya tabbatar da rasuwar Sarkin Katsinan Gusau, Mai Martaba Dr. Ibrahim Bello da safiyar ranar Juma'a, 25 ga Yuli, 2025.
Jami'an tsaro sun samu nasarar kashe wasu 'yan bindiga yayin wani artabu da suka yi a jihar Zamfara. Jami'an tsaron dai sun shirya musu kwanton bauna ne.
Mazauna wasu kauyukan Zamfara sun gudanar da zanga-zangar lumana domin nuna fushinsu kan hare-haren 'yan bindiga. Sun bukaci gwamnati ta kawo musu dauki.
Sojojin Operation Fansan Yamma sun kashe 'yan ta’adda da dama a Rijau, sun kwato bindigogi da babura 18, sai dai soja guda ya rasa ransa yayin fafatawa da maharan.
A labarin nan, za a ji cewa sojojin 'kasar nan sun yi nasarar fatattakar wasu 'yan ta'adda sama da 95 yayin suka baro Zamfara a babura zuwa Neja.
Rahotannin da muke samu sun tabbatar da cewa an samu gawar sanannen malamin addini, Malam Danladi Boss a wajen garin Dansaudau da ke karamar hukumar Maru a Zamfara.
Wasu 'yan bindiga dauke da makamai sun kai harin ta'addanci a jihar Zamfara. 'Yan bindigan sun hallaka manoma tare da sace dabbobi masu yawan gaske.
A wani mummunan harin yan bindiga, Hon. Muhammad Sala Wuta ya samu harbi a hannu da kafa yayin da yake kan hanyar zuwa Bukkuyum tare da wasu ’yan jam’iyya.
Jihar Zamfara
Samu kari