Siyasar Najeriya
Kudirin sauya fasalin harajin Shugaba Bola Tinubu na ci gaba da samun tangarɗa musamman a Arewacin Najeriya, mun haɗa maku ƴan siyasar da suka yi raddi.
Gwamnonin Arewa sun fara samun rabuwar kai kan kudirin haraji na Bola Ahmed Tinubu. Kano, Nasarawa da Benue sun nuna adawa, Benue, Kogi sun goyi baya.
Majalisar dokokin jihar Kano ta buƙaci sanatoci da ƴan majalisar wakilai na tarayya su haɗa kai su yaƙi sabon kudirin sauya fasalin harajin Bola Ahmed Tinubu.
Wani jigon PDP, David Itopa ya hango karshen gwamnatin Bola Tinubu idan jam'iyyun adawa suka hada kai. Itopa ya nuna kyakkyawan fata a kan hadewar Atiku da Obi.
Gwamna Babagana Umaru Zulum ya ce a nazarin da suka yi kan dokar sauya fasalin haraji, jihohin Legas da Ribas ne kaɗai za su amfani da yunƙurin Bola Tinubu.
An tattara jerin sunayen tsofaffin makiyan shugaban kasa Bola Tinubu wadanda a yanzu suka zama abokansa. Wannan ya nuna cewa siyasa ana yinta ba da gaba ba.
Sabon shugaban jam'iyyar APC na jihar Rivers, Tony Okocha, ya bayyana cewa muilkin jihar zai dawo hannunsu. Ya nuna cewa jam'iyyar za ta lashe zaben 2027.
Gwamnan jihar Ekiti ya bukaci ƴan siyasar da ke tura masa sakonni ta wayar tarho su dakata haka nan domin babu abin da zai faru sai da izinin Allah.
Babbar kotun tarayya mai zama a Abakaliki, babban birnin jihar Ebonyi ta halatta dakatarwar da aka yi wa mataimakin shugaban jam'iyyar PDP na ƙasa, Ali Odefa.
Siyasar Najeriya
Samu kari