Siyasar Arewa
Bayan Nasir El-Rufai ya bar APC zuwa SDP, jam'iyyar reshen jihar Kaduna ta bayyana cewa tsohon gwamna ba mambanta ba ne inda ta ba shi shawara da sauran al'umma.
Dan majalisar wakilai daga jihar Zamfara, Aminu Sani Jaji ya nesanta kansa daga wata makarkashiya da ake cewa ana kullawa don rage tasirin Sanata Abdulaziz Yari.
Malamin Musulunci a Kwara, Alfa Mohammed Ali Eyonbo Anabi, ya ce mahaifiyar Gwamna AbdulRazaq ta tabbatar musu tun 2019 cewa ɗanta zai yi kokari sosai a mulki.
Bayan korafin kiranye ga Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, Hukumar INEC ta ki amincewa da lamarin da cewa ba su cika sharudan da ya kamata ba bisa doka.
Shugaban jam'iyyar SDP na kasa, Shehu Musa Gabam ya ce sun shirya kwace mulki a hannun Bola Tinubu bayan tsofaffin Sanatoci da Ministoci sun koma SDP.
Yayin da SDP ke kara samun goyon baya, Malamin Musulunci, Imam Nura Gwanda ya jagoranci masu sauya sheka daga jam'iyyun APC da PDP zuwa SDP a Katsina.
Ministan harkokin jin-ƙai, ya ce PDP ba za ta ci gaba da mulki a Filato a 2027 ba domin APC ce za ta karbe jihar, kuma Shugaba Tinubu zai lashe zaɓen 2027 a Filato.
Tsohon ministan matasa na kasa, Solomon Dalung ya ce Remi Tinubu na bi Kiristocin Arewa tana cewa Musulman Arewa sun juya baya ga Bola Tinubu kan 2027.
Shugaban SDP a Najeriya, Shehu Musa Gabam ya ziyarci 'yar takarar gwamna a APC a Adamawa, Aishatu Dahiru Binani. Gabam ya bukaci mata su shiga SDP.
Siyasar Arewa
Samu kari