Shugaban Sojojin Najeriya
Rundunar sojin Najeriya ta ceto wasu mutane 21 da 'yan bindiga suka sace a jihohin Kwara da Kogi. Dakarun sojin sun bayyana cewa wasu daga cikinsu sun kasa tafiya.
Sojojin Najeriya sun kama kwamandan IPOB/ESN, Ifeanyi Eze (Gentle De Yahoo) a Imo, tare da wata mata mai taimakawa kungiyar, an gano makamai, mota da yara.
A labarin nan, za a ji cewa gwamnatin jihar Kebbi ta baza komarta zuwa kasar Sin domin ta fatattaki Lakurawa a kokarinta na dawo da zaman lafiya sassan jihar.
Rundunar tsaron Najeriya ta bayyana shirin murkushe kungiyar 'yan ta'addan Wulowulo da aka ce tsagin Boko Haram ne da ta bulla a Arewa ta Tsakiyan Najeriya.
Sojojin JTF sun kama ma’aurata da ake zargi da safarar makamai zuwa ‘yan ta’adda a Kaduna, sun gano harsasai 1,207 da ake shirin kaiwa Arewa maso Yamma.
A labarin nan, za a ji cewa an yi ba ta kashi a tsakanin sojojin Najeriya da miyagun 'yan bindiga jim kadan bayan an kammala yarjejeniyar zaman lafiya a Katsina.
A labarin nan nan, za a ji cewa shahararren mai garkuwa da mutanen nan, Kelvin Oniarah Ezigbe, da ya sace fitaccen lauya, Mike Mike Ozekhome (SAN) ya samu sassauci.
Shugaba Bola Tinubu ya rage hukuncin daurin rai da rai ga tsohon hafsan soja Suleiman Akubo da aka kama da sayar da makamai ga ‘yan tawayen Neja Delta.
A wani sojan Najeriya ya kashe kan shi tare da harbe matar shi har lahira. Rundunar sojin Najeriya za ta cigaba da bincike kuma za ta dauki mataki kan lamarin.
Shugaban Sojojin Najeriya
Samu kari