Rikicin PDP
Kusoshin PDP a Arewa ta Tsakiya za su nada shugaban riko na kasa daga yankin. Shugabanni sun yi kira ga hadin kai da bin kundin tsarin PDP don ci gaba.
Masu ruwa da tsakin PDP a shiyyar Arewa ta Tsakiya sun jaddada cewa suna nan a kan bakarsu ta samar da wanda zai maye gurbin shugaban jam'iyya, Damagum.
Rigimar cikin gida a PDP ta kara ƙamari yayin da shugabannin gunduma suka sanar da korar mataimakin shugaban jam'iyya na Kusu maso Gabas, Ali Odefa.
Kusa a PDP ya yi zargin Nyesom Wike ya zamarwa jam'iyyar karfen kada. Tonye Cole ya ce Wike ya karbo kwangilar rusa PDP. Ya yi mamakin yadda aka kasa daukar mataki.
Jam'iyyar APC ta wanke kanta daga zargin cewa ta jefa rikici a PDP. APC ta yi wa Atiku zazzafan martani kan cewa tana amfani da Wike wajen hura wuta a PDP.
Paul Ibe, mai magana da yawun tsohon mataimakin shugaban ƙasa ya ce haɗa kan maoi gidansa Atiku Abubakar da Peter Obi zai kawo karshen mulkin APC.
Duyar tsohon gwamnan jihar Delta, Erhiatake Ibori-Suenu ta bayyana cewa babu wata doka da ta haramta nata barin jam'iyyar PDP zuwa APC mai mulkin ƙasar nan.
Babbbar jam'iyyar adawa reshen jihar Imo a Kudu maso Yamma ta kori ɗan majalisar wakilan tarayya, Imo Ugochinyere Ikeagwonu bisa zargin rashin ɗa'a.
Kwamitin amintattu na PDP ya nuna damuwarsa kan rashin gudanar da taron NEC na jam'iyyar. Kwamitin na son ganin an kawo karshen rikicin da ya addabi PDP.
Rikicin PDP
Samu kari