Rikicin PDP
Tsohon gwamnan jihar Sokoto a Najeriya, Dalhatu Attahiru Bafarawa, ya sanar da ficewar shi daga babbar jam'iyyar adawa ta ƙasar - PDP. Tsohon gwamnan ya fadi dalili.
Jam'iyyar PDP reshen jihar Ebonyi ta zaɓi Chidiebere Egwu a matsayin wanda zai maye gurbin mataimakin shugabanta na dhiyyar Kudu maso Gabas, Ali Odefa.
Tsohon mai magana da yawun PDP na ƙasa, Kola Ologbodiyan ya ce akwai wasu daga APC da ke yunƙurin ganin bayan babbar jam'iyyar adawa, ya ce dole su tashi tsaye.
Shugaban PDP a jihar Abia, Hon Abraham Amah ya katyata rahoton da ke yawo cewa Ƴam majalisa 12 na shirin ficewa daga jam'iyyar zuwa wata, ya ce abin dariya ne.
Babbar kotun Ribas mai zama a Fatakwal ta soke tarukan zaɓen shugabannin PDP da aka gudanar a jihar Ribas a watan Yulin, 2024, ta ce an saɓawa doka.
Sanata Samuel Anyanwu ya koma bakin aiki a matsayin sakataren jam'iyyar PDP na kasa. Anyanwu ya ce ya daukaka kara kan hukuncin kotu da ya sauke shi.
'Yan sanda sun mamaye hedikwatar PDP a Abuja bayan rikicin jam'iyyar PDP ya yi kamari. An samu sakatarorin jam'iyyar PDP biyu bayan hukuncin kotu.
PDP ta ce ta shirya domin kwace mulkin Najeriya a 2027. Sakataren jam'iyyar ya ce suna hade waje daya karkashin jagorancon Umar Damagun a fadin kasa baki daya.
Jam’iyyar PDP a jihar Akwa Ibom ta zabi Gwamna Umo Eno a matsayin dan takararta tilo na zaben gwamna na shekarar 2027 inda ta haramta wa sauran yan takara.
Rikicin PDP
Samu kari