Jihar Oyo
Shugaban jam'iyyar APC na kasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya tarbi wani jigoɓda ya dawo APC a jihar Oyo. Ya bayyana cewa jam'iyyar za ta kwato Osun, Oyo a hannun PDP.
An sake samun wani da yake ikrarin shi Annabi ne kuma yana ganin Allah. A karyarsa, ya ce shi ya fi Annabi Musa kuma ya taba ganin Allah da idonsa ba labari ba.
Rahotanni sun tabbatar da cewa an yi asarar rayukan mutane 22 a waus haɗurran motoci da suka afku a jihohin Kogi, Oyo da Ogun, wasu sun samu rauni.
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde ya amince da sake naɗin Prince Adebayo Adegbola a matsayin sarkin Eruwa bayan shafe shekaru biyr da stige shi daga sarauta.
Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo ya bayyana cewa a watan Janairu, 2026 sanar da ɗan takarar da yake goyon bayan ya gaji kujerarsa a babban zaben 2027.
Bayan yada jita-jitar cewa Olubadan ya riga mu gidan gaskiya, Gwamnatin Oyo ta mayar da martani kan rade-radin inda ta ce babu kamshin gaskiya kan mutuwar basarake.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana jimami da alhini bisa rasuwar shugaban majalisar sarakunam Arewa da ke Kudu, Alhaji Haruna Maiyasin Katsina.
Rahotanni sun tabbatar da cewa an birne Sarkin Sasa, Haruna Maiyasin Katsina, wanda ya rasu yana da shekara 125, a gidansa da ke Sasa, Ibadan, Oyo a yau Lahadi.
Makinde ya jajanta wa iyalan Sarkin Sasa, yana mai cewa rasuwarsa babban rashi ne ga al’ummar Hausa/Fulani, ya kuma yi masa addu’ar samun Aljanna Firdausi.
Jihar Oyo
Samu kari