Matasan Najeriya
Mukaddashin gwamnan jihar Katsina, Malam Faruk Lawal Jobe, ya bayar da izinin sassauta dokar hana zirga-zirga ta sa’o’i 24 a karamar hukumar Dutsinma.
Yayin da aka shiga rana ta shida a cigaba da zanga-zanga, wasu mazauna Kano sun koka kan yadda kayan masarufi da abinci suka yi wahalar samu a birnin.
Rahotanni sun tabbatar da cewa jami'an tsaro sun bindige wani mai zanga-zanga a karamar hukumar Katagum a jihar Bauchi yayin da ake cigaba da hawa tituna a Najeriya.
Wani faifan bidiyo ya nuna yadda wani jami'in tsaro ya sa bindiga ya harbe mataahin da ya fito zanga zanga har lahira a jihar Bauchi ranar Litinin 5 ga wata.
Zanga zanga ta ɗauki sabon salo a jihar Osun da ma wasu sassan Najeriya a rana ta biyar watau yau Litinin, 5 ga watan Agusta, 2024 yayin da wasu suka fara cire kaya.
Bola Tinubu ya sha suka kan jawabin da ya gudanar a jiya Lahadi 4 ga watan Agustan 2024 inda suka ce bai yi magana kan bukatun masu zanga-zanga ba.
Gweamnatin Kano ta dauki matakai shida na ganin ta magance matsalolin masu zanga-zanga yayin da kuma ta yi magana kan daga turar Rasha da aka yi a jihar.
Ofishin jakadancin ƙasar Rasha a Najeriya ya nesanta gwamnatin ƙasar daga zargin hannu a ɗaga tutocinta da masu zanga zanga ke yi musamman a jihohin Arewa.
Tun fara zanga zangar adawa da tsadar rayuwa a Najeriya an samu muhimman abubuwa da suka ja hankalin al'umma wanda suka hada da daga tutar Rasha da jawabin Tinubu.
Matasan Najeriya
Samu kari