Masu Garkuwa Da Mutane
'Yan bindigan da ake zargin sun tsere ne daga daga yankunan Bakura - Talata Mafara na jihar Zamfara, sun kai hari ƙaramar hukumar Dange Shuni a Sokoto sun sace
Sakamakon musayar ruwan wuta tsakanin miyagun 'yan bindigan daji da 'yan banga da aka yi a yankin Mayaki da ke karamar Lapai ta Niger, 'yan banga 2 sun rasu.
Shugabannin 'yan bindiga masu tarin yawa da yaransu sun sheka barzahu a yayin luguden wutan da ake yi a jihar Zamfara, majiyoyi masu tarin yawa suke sanarwa.
Wata majiyar da ta bukaci a sakaya sunanta ta ce, an yi awon gaba da tsohon Sanatan ne a cikin wata mota kirar Toyota Camry zuwa wani waje da ba a sani ba.
Masu garkuwa da mutane don kudin fansa sun sace Cif Gbalipre Turner, mahaifi ga Shugaban Karamar Hukumar Ogbia ta Jihar Bayelsa, Hon. Ebinyo Marvin Turner.
Samaila Dahiru, dalibin GDSS Kaya, ya bayyana yadda ‘yan bindigan da suka yi yunkurin halaka malaminsa suka harbe shi amma kuma ya tsira, The Cable ta ruwaito.
Masu garkuwa da mutane sun sace wata Mrs Oladapo Bukola mai shekaru 45 da yaranta 2 a wuraren Pegi dake Kuje a Abuja.Bayan kwana 2 da sace wani Abdullahi Benda.
Rundunar hukumar ‘yan sanda na musamman tare da hadakar sauran jami’an ta mayar da farmakin da daruruwan ‘yan bindiga suka kai garin Shinkafi, a jihar Zamfara.
Anyi awon gaba da wani mahaifi, Abdullahi Benda, da dansa mai shekaru 23, Jibrin Abdullahi Benda a gidansu da ke kauyen Yangoji a karamar hukumar Kwali ta Abuja
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari