Masu Garkuwa Da Mutane
Mahara sun kai sabon hari kauyen Baka, karamar hukumar Igabi da ke jihar Kaduna, inda suka kashe uba da dansa a safiyar ranar Asabar, 13 ga watan Fabrairu.
Gwamnan Zamfara, Bello Matawalle ya sha bam-bam da Gwamna Nasir El-Rufai kan batun rashin tsaro. Yace ta sulhu ne za a kawo zaman lafiya cikin sauki a Zamfara.
Wasu yan bindiga a ranar Laraba, 10 ga watan Fabrairu sun kai farmaki tashar bincike na yan sanda da ke karamar hukumar Takum, jihar Taraba, sun kashe jami'i 1.
'Yan Majalisar sun bada shawara ayi wa tsarin tsaro na kasar garambawul. Anyi kira ga Jami’an tsaro su tura jirage su tsefe dajin da ‘yan bindiga su ke fake.
Dakarun sojin saman Najeriya sun halaka 'yan bindiga masu tarin yawa a samamen da suka kai ta jiragen yakin soja a karamar hukumar Birnin Gwari ta jihar Kaduna.
Mataimakin shugaban kasa yemi Osinbajo ya ce nada sabbin hafsoshin tsaro da gwamnatin tarayya tayi yasa an samar da sabbin dabaru da hanyoyin yakar ta'addanci.
Shugaban kasa ya bukaci hafsun sojoji su murkushe ‘Yan ta’addan Boko Haram. Buhari da Minista sun bukaci a samu hadi-kai tsakanin dakarun sama da kuma na kasa.
Wasu da ake zaton masu garkuwa da mutane ne a ranar Talata, 9 ga watan Fabarairu sun yi garkuwa da hadimin mataimakin gwamnan jihar Taraba, Alhaji Bala Baba.
Yan banga na unguwa a Dutsen Abba da ke karamar hukumar Zaria sun kama wasu mutane uku da ake zargin yan leken asirin yan bindiga ne, Daily Trust ta ruwaito. Mu
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari